< Numbers 8 >
1 Adonai spoke to Moses [Drawn out], saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Speak to Aaron [Light-bringer], and tell him, ‘When you light the menorah ·lamp· candles, the seven menorah ·lamp· candles shall give light in front of the menorah ·lamp·.’”
“Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
3 Aaron [Light-bringer] did so. He lit its menorah ·lamp· candles to light the area in front of the menorah ·lamp·, as Adonai enjoined Moses [Drawn out].
Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
4 This was the workmanship of the menorah ·lamp·, beaten work of gold. From its base to its flowers, it was beaten work: according to the pattern which Adonai had shown Moses [Drawn out], so he made the menorah ·lamp·.
Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
5 Adonai spoke to Moses [Drawn out], saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 “Take the Levites [Descendants of United with] from among the children of Israel [God prevails], and cleanse them.
“Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
7 You shall do this to them, to cleanse them: sprinkle the water of habitual sin ·missing the mark· cleansing on them, let them shave their whole bodies with a razor, and let them wash their clothes, and cleanse themselves.
Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
8 Then let them take a young bull, and its meal offering, fine flour mixed with oil; and another young bull you shall take for a habitual sin ·miss the mark· offering.
Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
9 You shall present the Levites [Descendants of United with] before the Tent of Meeting. You shall assemble the whole congregation of the children of Israel [God prevails].
Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
10 You shall present the Levites [Descendants of United with] before Adonai. The children of Israel [God prevails] shall lay their hands on the Levites [Descendants of United with],
Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
11 and Aaron [Light-bringer] shall offer the Levites [Descendants of United with] before Adonai for a wave offering, on the behalf of the children of Israel [God prevails], that it may be theirs to do the service of Adonai.
Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
12 “The Levites [Descendants of United with] shall lay their hands on the heads of the bulls, and you shall offer the one for a habitual sin ·miss the mark· offering, and the other for a burnt offering to Adonai, to make atonement for the Levites [Descendants of United with].
“Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
13 You shall set the Levites [Descendants of United with] before Aaron [Light-bringer], and before his sons, and offer them as a wave offering to Adonai.
Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
14 Thus you shall separate the Levites [Descendants of United with] from among the children of Israel [God prevails], and the Levites [Descendants of United with] shall be mine.
Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
15 “After that, the Levites [Descendants of United with] shall go in to do the service of the Tent of Meeting: and you shall cleanse them, and offer them as a wave offering.
“Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
16 For they are wholly given to me from among the children of Israel [God prevails]; instead of all who open the womb, even the firstborn of all the children of Israel [God prevails], I have taken them to me.
Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
17 For all the firstborn among the children of Israel [God prevails] are mine, both man and animal. On the day that I struck all the firstborn in the land of Egypt [Abode of slavery], I sanctified them for myself.
Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
18 I have taken the Levites [Descendants of United with] instead of all the firstborn among the children of Israel [God prevails].
Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
19 I have given the Levites [Descendants of United with] as a gift to Aaron [Light-bringer] and to his sons from among the children of Israel [God prevails], to do the service of the children of Israel [God prevails] in the Tent of Meeting, and to make atonement for the children of Israel [God prevails]; that there be no plague among the children of Israel [God prevails], when the children of Israel [God prevails] come near to the sanctuary.”
Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
20 Moses [Drawn out], and Aaron [Light-bringer], and all the congregation of the children of Israel [God prevails] did so to the Levites [Descendants of United with]. According to all that Adonai enjoined Moses [Drawn out] concerning the Levites [Descendants of United with], so the children of Israel [God prevails] did to them.
Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 The Levites [Descendants of United with] cleansed sin ·err (the standard goal)· from themselves from sin, and they washed their clothes; and Aaron [Light-bringer] offered them for a wave offering before Adonai; and Aaron [Light-bringer] made atonement for them to cleanse them.
Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
22 After that, the Levites [Descendants of United with] went in to do their service in the Tent of Meeting before Aaron [Light-bringer], and before his sons: as Adonai had enjoined Moses [Drawn out] concerning the Levites [Descendants of United with], so they did to them.
Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
23 Adonai spoke to Moses [Drawn out], saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
24 “This is that which belongs to the Levites [Descendants of United with]: from twenty-five years old and upward they shall go in to wait on the service in the work of the Tent of Meeting;
“Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
25 and from the age of fifty years they shall cease waiting on the work, and shall serve no more,
amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
26 but shall minister with their brothers in the Tent of Meeting, to perform the duty, and shall do no service. You shall do thus to the Levites [Descendants of United with] concerning their duties.”
Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”