< John 1 >

1 B'resheet ·In the beginning of the beginning· was ha D'var ·the Word·, and ha D'var ·the Word· was with God, and ha D'var ·the Word· was God.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 The same was in the beginning with God.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 All things came to be through him and without him nothing made had being.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 In him was life, and the life was the light of men.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 The light shines in the darkness, and the darkness has not overcome it.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 There came a man, sent from God, whose name was John [Yah is gracious].
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 The same came as a witness, that he might testify about the light, that all might believe through him.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 He was not the light, but was sent that he might testify about the light.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 The true light that enlightens everyone was coming into the world.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 He was in the world, and the world was made through him, and the world didn’t recognize him.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 He came to his own, and those who were his own didn’t receive him.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 But as many as received him, to them he gave the right to become God’s children, to those who believe in his name:
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 who were born not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 Ha D'var ·The Word· became flesh, and tabernacled among us. We saw his shekhinah ·manifest weighty glory and presence of God·, such shekhinah ·manifest weighty glory and presence of God· as of the one and only Son of the Abba ·Father·, full of grace and truth.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 John [Yah is gracious] testified about him. He cried out, saying, “This was he of whom I said, ‘He who comes after me has surpassed me, for he was before me.’”
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 From his fullness we all received grace upon grace.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 For the Torah ·Teaching· was given through Moses [Drawn out]; grace and truth came through Yeshua Messiah [Salvation Anointed one].
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 No one has seen God at any time. The one and only Son, who is in the bosom of Abba ·Father familiar, Dear Dad·, he has declared him.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 This is John [Yah is gracious]’s testimony, when the Jews sent priests and Levites [Descendants of United with] from Jerusalem [City of peace] to ask him, “Who are you?”
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 He declared, and didn’t deny, but he declared, “I am not the Messiah [Anointed one].”
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 They asked him, “What then? Are you Elijah [My God Yah]?” He said, “I am not.” “Are you the prophet?” He answered, “No.”
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 They said therefore to him, “Who are you? Give us an answer to take back to those who sent us. What do you say about yourself?”
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 He said, “I am the voice of one crying in the wilderness, ‘Make straight the way of MarYah [Master Yahweh],’ as Isaiah [Salvation of Yah] the prophet said.”
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 The ones who had been sent were from the Pharisees [Separated].
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 They asked him, “Why then do you baptize, if you are not the Messiah [Anointed one], nor Elijah [My God Yah], nor the prophet?”
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 John [Yah is gracious] answered them, “I baptize in water, but among you stands one whom you don’t know.
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 He is the one who comes after me, who is preferred before me, whose sandal strap I’m not worthy to loosen.”
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 These things were done in Bethany [House of affliction] beyond the Jordan [Descender], where John [Yah is gracious] was baptizing.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 The next day, he saw Yeshua [Salvation] coming to him, and said, “Behold, the Lamb of God, who takes away the sin of the world!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 This is he of whom I said, ‘After me comes a man who is preferred before me, for he was before me.’
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 I didn’t know him, but for this reason I came baptizing in water: that he would be revealed to Israel [God prevails].”
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 John [Yah is gracious] testified, saying, “I have seen haRuach [the Spirit] descending like a dove out of heaven, and it remained on him.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 I didn’t recognize him, but he who sent me to baptize in water, he said to me, ‘On whomever you will see haRuach [the Spirit] descending, and remaining on him, the same is he who baptizes in Ruach haKodesh [Spirit of the Holiness].’
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 I have seen, and have testified that this is the Ben-Elohim ·Son of Elohim God·.”
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Again, the next day, John [Yah is gracious] was standing with two of his disciples,
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 and he looked at Yeshua [Salvation] as he walked, and said, “Behold, the Lamb of God!”
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 The two disciples heard him speak, and they followed Yeshua [Salvation].
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 Yeshua [Salvation] turned, and saw them following, and said to them, “What are you looking for?” They said to him, “Rabbi ·Teacher·” (which is to say, being interpreted, Teacher), “where are you staying?”
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 He said to them, “Come, and see.” They came and saw where he was staying, and they stayed with him that day. It was about four o'clock in the afternoon.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 One of the two who heard John [Yah is gracious], and followed him, was Andrew [Manly], Simeon Peter [Hearing Rock]’s brother.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 He first found his own brother, Simeon [Hearing], and said to him, “We have found the Messiah [Anointed one]!” (which is, being interpreted, Moshiach ·Anointed one·).
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 He brought him to Yeshua [Salvation]. Yeshua [Salvation] looked at him, and said, “You are Simeon [Hearing] the son of Jonah [Dove]. You shall be called Cephas” (which is by interpretation, Peter [Rock]).
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 On the next day, he was determined to go out into Galilee [District, Circuit], and he found Philip [Loves horses]. Yeshua [Salvation] said to him, “Follow me.”
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Now Philip [Loves horses] was from Bethsaida, of the city of Andrew [Manly] and Peter [Rock].
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Philip [Loves horses] found Nathanael [Given by God], and said to him, “We have found the one that Moses [Drawn out] wrote about in the Torah ·Teaching·, and the Prophets— it is Yeshua [Salvation] son of Joseph [May he add] from Nazareth [Branch, Separated one].”
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Nathanael [Given by God] said to him, “Can any good thing come out of Nazareth [Branch, Separated one]?” Philip [Loves horses] said to him, “Come and see.”
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Yeshua [Salvation] saw Nathanael [Given by God] coming to him, and said about him, “Behold, an Israelite [Descendant of God prevails] indeed, in whom is no deceit!”
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Nathanael [Given by God] said to him, “How do you know me?” Yeshua [Salvation] answered him, “Before Philip [Loves horses] called you, when you were under the fig tree, I saw you.”
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Nathanael [Given by God] answered him, “Rabbi ·Teacher·, you are the Ben-Elohim ·Son of Elohim God·! You are Melek Isra'el [King of God prevails]!”
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 Yeshua [Salvation] answered him, “Because I told you, ‘I saw you underneath the fig tree,’ do you believe? You will see greater things than these!”
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 He said to him, “Most certainly, I tell you, hereafter you will see heaven opened, and the angels of God ascending and descending on the Son of Man.”
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”

< John 1 >