< Deuteronomy 11 >

1 Therefore you shall 'ahav ·affectionately love· Adonai your God, and keep his instructions, his statutes, his judgments, and his mitzvot ·instructions·, always.
To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
2 Know this day: for I don’t speak with your children who have not known, and who have not seen the chastisement of Adonai your God, his greatness, his mighty hand, his outstretched arm,
Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
3 his signs, and his works, which he did in the middle of Egypt [Abode of slavery] to Pharaoh the king of Egypt [Abode of slavery], and to all his land;
alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
4 and what he did to the army of Egypt [Abode of slavery], to their horses, and to their chariots; how he made the water of the Sea of Suf [Reed Sea] to overflow them as they pursued you, and how Adonai has destroyed them to this day;
ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
5 and what he did to you in the wilderness, until you came to this place;
Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
6 and what he did to Dathan and Abiram, the sons of Eliab, the son of Reuben [See, a son!]; how the earth opened its mouth, and swallowed them up, and their households, and their tents, and every living thing that followed them, in the middle of all Israel [God prevails];
ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
7 but your eyes have seen all of Adonai’s great work which he did.
Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
8 Therefore you shall keep every mitzvah ·instruction· which I enjoin you today, that you may be strong, and go in and possess the land, where you go over to possess it;
Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
9 and that you may prolong your days in the land, which Adonai swore to your fathers to give to them and to their offspring, a land flowing with milk and honey.
domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
10 For the land, where you go in to possess it, is not as the land of Egypt [Abode of slavery], that you came out of, where you sowed your seed, and watered it with your foot, as a garden of herbs;
Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
11 but the land, where you go over to possess it, is a land of hills and valleys which drinks water from the rain of the sky,
Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
12 a land which Adonai your God cares for. Adonai your God’s eyes are always on it, from the beginning of the year even to the end of the year.
Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
13 It shall happen, if you shall sh'ma ·hear obey· diligently to my mitzvot ·instructions· which I enjoin you today, to 'ahav ·affectionately love· Adonai your God, and to abad ·serve· him with all your heart and with all your soul,
Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
14 that I will give the rain of your land in its season, the former rain and the latter rain, that you may gather in your grain, your new wine, and your oil.
sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
15 I will give grass in your fields for your livestock, and you shall eat and be full.
Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
16 Be careful, lest your heart be deceived, and you turn aside, and abad ·serve· other deities, and hawa ·bow low, prostrate· to worship them;
Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
17 and Adonai’s anger be kindled against you, and he shut up the sky, so that there is no rain, and the land does not yield its fruit; and you perish quickly from off the good land which Adonai gives you.
don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
18 Therefore you shall lay up these my words in your heart and in your soul. You shall bind them for a sign on your hand, and they shall be for frontlets between your eyes.
Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
19 You shall teach them your children, talking of them, when you sit in your house, and when you walk by the way, and when you lie down, and when you rise up.
Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
20 You shall write them on the door posts of your house, and on your gates;
Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
21 that your days may be multiplied, and the days of your children, in the land which Adonai swore to your fathers to give them, as the days of the heavens above the earth.
saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
22 For if you shall diligently keep all these mitzvot ·instructions· which I enjoin you, to do them, to 'ahav ·affectionately love· Adonai your God, to walk in all his ways, and to dabak ·cling to, worship· to him;
In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
23 then will Adonai drive out all these nations from before you, and you shall dispossess nations greater and mightier than yourselves.
Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
24 Every place whereon the sole of your foot treads shall be yours: from the wilderness, and Lebanon, from the river, the river Euphrates [Fruitful], even to the western sea shall be your border.
Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
25 No man will be able to stand before you. Adonai your God will lay the fear of you and the dread of you on all the land that you tread on, as he has spoken to you.
Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
26 Behold, I set before you today a blessing and a curse:
Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
27 the blessing, if you sh'ma ·hear obey· the mitzvot ·instructions· of Adonai your God, which I enjoin you today;
albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
28 and the curse, if you do not sh'ma ·hear obey· the mitzvot ·instructions· of Adonai your God, but turn aside out of the way which I enjoin you today, to go after other deities, which you have not known.
la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
29 It shall happen, when Adonai your God brings you into the land where you go to possess it, that you shall set the blessing on Mount Gerizim, and the curse on Mount Ebal.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
30 Are not they beyond the Jordan [Descender], behind the way of the going down of the sun, in the land of the Canaanites [Descendants of Humbled] who dwell in the Arabah, near Gilgal, beside the oaks of Moreh?
Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
31 For you are to pass over the Jordan [Descender] to go in to possess the land which Adonai your God gives you, and you shall possess it, and dwell therein.
Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
32 You shall observe to do all the statutes and the judgments which I set before you today.
ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.

< Deuteronomy 11 >