< Zechariah 2 >

1 I lifted up mine eyes again, and looked, and behold, a man with a measuring-line in his hand.
Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
2 Then said I, Whither goest thou? And he said to me, To measure Jerusalem, to see what is the breadth thereof, and what is the length thereof.
Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
3 And behold, the angel who talked with me went forth, and another angel went forth to meet him,
Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
4 and said to him, Run, speak to that young man, saying: Jerusalem shall be inhabited without walls On account of the multitude of men and of cattle within her.
ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
5 And I will be to her, saith Jehovah, A wall of fire round about, And glory will I be within her.
Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
6 Ho! ho! flee ye out of the land of the North, saith Jehovah; For toward the four winds of heaven have I scattered you abroad, saith Jehovah.
“Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
7 Ho, Zion, escape, Thou that dwellest with the daughter of Babylon!
“Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
8 For thus saith Jehovah of hosts: For glory hath he sent me to the nations which plundered you; (For he that toucheth you toucheth the apple of his eye.)
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
9 For, behold, I will shake my hand over them, And they shall be a spoil to those that served them; And ye shall know that Jehovah of hosts hath sent me.
Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
10 Sing and rejoice, O daughter of Zion! For, behold, I will come, And I will dwell in the midst of thee, saith Jehovah;
“Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
11 And many nations shall join themselves to Jehovah in that day, And shall be my people; And I will dwell in the midst of thee; And thou shalt know that Jehovah of hosts hath sent me to thee.
“Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
12 And Jehovah will possess Judah as his portion in the holy land, And will again choose Jerusalem.
Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
13 Be silent, all flesh, before Jehovah! For he riseth up from his holy habitation.
Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”

< Zechariah 2 >