< Psalms 95 >
1 O come, let us sing to the LORD; Let us raise a voice of joy to the rock of our salvation!
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Let us come into his presence with thanksgiving, And sing joyfully to him with psalms!
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For Jehovah is a great God; Yea, a great king over all gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 In his hands are the depths of the earth; His also are the heights of the mountains.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 The sea is his, and he made it; The dry land also his hands formed.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 O come, let us worship and bow down! Let us kneel before the LORD, our maker!
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 For he is our God, And we are the people of his pasture and the flock of his hand. O that ye would now hear his voice!
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 “Harden not your hearts as at Meribah [[the strife]], As in the day of temptation [[Massah]] in the wilderness,
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 Where your fathers tempted me And tried me, although they had seen my works.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Forty years was I offended with that generation: And I said, 'They are a people of a perverse heart, And who have no regard to my ways.'
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 Therefore I sware, in my wrath, That they should not enter into my rest.”
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”