< Psalms 87 >

1 “A psalm of the sons of Korah.” His foundation is in the holy mountains;
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 Jehovah loveth the gates of Zion More than all the dwellings of Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Glorious things are said of thee, O city of God! (Pause)
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 “I name Egypt and Babylon among them that know me; Behold! Philistia, Tyre, and Ethiopia, —They also were born there.”
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 And of Zion it shall be said, “Men of every nation were born there, And the Most High hath established her.”
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 Jehovah, when he numbereth the nations, shall write, “These were born there!” (Pause)
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 Singers as well as dancers, —All my springs are in thee!
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”

< Psalms 87 >