< Psalms 83 >
1 “A psalm of Asaph.” O God! keep not silence! Hold not thy peace, and be not still, O God!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For, lo! thine enemies roar, And they who hate thee lift up their heads.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 For they form secret plots against thy people, And consult together against thy chosen ones.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 “Come,” say they, “let us blot them out from the number of the nations, That the name of Israel may no more be remembered!”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 With one consent they consult together, Against thee do they form a league, —
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 The tents of Edom and the Ishmaelites, Of Moab and the Hagarenes,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal and Ammon and Amalek, The Philistines, with the inhabitants of Tyre.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 The Assyrians also are joined with them; They lend their strength to the children of Lot.
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do to them as to the Midianites, As to Sisera, as to Jabin at the brook Kison,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Who perished at Endor, And were trampled like dung to the earth.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their chiefs like Oreb and Zeeb; Yea, all their princes as Zeba and Zalmunna!
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Who say, “Let us seize on God's habitations!”
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Make them, O my God! like whirling chaff; Like stubble before the wind!
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As fire consumeth the forest, And as flame setteth the mountains in a blaze,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 So pursue them with thy tempest, And terrify them with thy storm!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Cover their faces with shame, That they may seek thy name, O LORD!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Let them be confounded! Yea, let them be put to shame, and perish!
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 That they may know that thy name alone is Jehovah; That thou art the Most High over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.