< Psalms 77 >
1 “For the leader of the music of the Jeduthunites. A psalm of Asaph.” I call upon God; I cry aloud for help; I call upon God, that he would hear me!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In the day of my trouble I seek the Lord; In the night is my hand stretched forth continually; My soul refuseth to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I remember God, and am disquieted; I think of him, and my spirit is overwhelmed.
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Thou keepest mine eyelids from closing; I am distressed, so that I cannot speak!
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I think of the days of old, —The years of ancient times.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 I call to remembrance my songs in the night; I meditate in my heart, And my spirit inquireth:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Will the Lord be angry for ever? Will he be favorable no more?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Is his mercy utterly withdrawn for ever? Doth his promise fail from generation to generation?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Hath God forgotten to be gracious? Hath he in anger shut up his compassion?
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Then I say, “This is mine affliction, A change in the right hand of the Most High.”
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I remember the deeds of Jehovah; I think of thy wonders of old.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 I meditate on all thy works, And talk of thy doings.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Thy ways, O God! are holy! Who so great a god as our God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Thou art a God who doest wonders; Thou hast manifested thy power among the nations.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 With thy strong arm thou didst redeem thy people, —The sons of Jacob and Joseph.
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters saw thee, O God! The waters saw thee, and feared, And the deep trembled.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 The clouds poured out water, The skies sent forth thunder, And thine arrows flew.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 Thy thunder roared in the whirlwind; Thy lightning illumined the world; The earth trembled and shook.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Thy way was through the sea, And thy path through great waters; And thy footsteps could not be found.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Thou didst lead thy people like a flock, By the hands of Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.