< Psalms 27 >
1 “A psalm of David.” The LORD is my light and my salvation; Whom shall I fear? The LORD is the shield of my life; Of whom shall I be afraid?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 When the wicked came upon me to devour me, Even my persecutors and enemies, they stumbled and fell.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Though a host should encamp against me, my heart shall not fear; Though war should rise against me, yet will I be confident.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 One thing have I desired of the LORD; that do I yet seek; That I may dwell in the house of the LORD all the days of my life, To behold the grace of the LORD, And to gaze upon his temple.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 For in the day of trouble he will hide me in his pavilion; Yea, in the secret place of his tabernacle will he shelter me; He will set me upon a rock.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 Yea, already doth he lift my head above my enemies, who are around me; Therefore in his tabernacle will I offer sacrifices with the sound of trumpets; I will sing, yea, with instruments of music I will give praise to the LORD.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Hear my voice, O LORD! when I cry unto thee; Have pity upon me, and answer me!
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 When I think of thy precept, “Seek ye my face!” Thy face, LORD, do I seek.
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 O hide not thou thy face from me; Cast not thy servant away in displeasure! Thou hast been my help, do not leave me; Do not forsake me, O God, my helper!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 For my father and my mother have forsaken me; But the LORD will take me up.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Teach me thy way, O LORD! And lead me in the right path, because of my enemies!
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Give me not up to the will of my adversaries! For false witnesses have risen up against me, And such as breathe out injustice.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 I trust that I shall see the goodness of the LORD In the land of the living. Hope thou in the LORD!
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Be of good courage; let thy heart be strong; Hope thou in the LORD!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.