< Psalms 24 >
1 “A psalm of David.” The earth is the LORD'S, and all that is therein; The world, and they who inhabit it.
Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
2 For he hath founded it upon the seas, And established it upon the floods.
gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
3 Who shall ascend the hill of the LORD? And who shall stand in his holy place?
Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
4 He that hath clean hands and a pure heart; Who hath not inclined his soul to falsehood, Nor sworn deceitfully.
Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
5 He shall receive a blessing from the LORD, And favor from the God of his salvation.
Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
6 This is the race of them that seek him; They that seek thy face are Jacob. (Pause)
Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
7 Lift up your heads, O ye gates! Lift yourselves up, ye everlasting doors, That the king of glory may come in!
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
8 “Who is this king of glory?” Jehovah, strong and mighty; Jehovah, mighty in battle.
Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
9 Lift up your heads, O ye gates! Lift yourselves up, ye everlasting doors, That the king of glory may enter in!
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
10 “Who is this king of glory?” Jehovah, God of hosts, he is the king of glory. (Pause)
Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)