< Psalms 22 >

1 “For the leader of the music. To the tune of “The hind of the morning.” A psalm of David.” My God, my God! why hast thou forsaken me? Why so far from mine aid, and from the words of my cry?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 O my God! I cry during the day, but thou hearest not; In the night also, but I have no rest.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 And yet thou art holy, Dwelling amid the praises of Israel!
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Our fathers trusted in thee; They trusted, and thou didst save them.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 They called upon thee, and were delivered; They trusted in thee, and were not put to shame.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 But I am a worm, and not a man; The reproach of men, and the scorn of the people.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 All who see me scoff at me; They open wide the lips; they shake the head.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 “He trusted in the LORD, let him help him; Let him deliver him, since he delighted in him!”
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Surely thou art he that didst bring me into the world; Thou didst make me lie secure upon my mother's breast!
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Upon thee have I cast myself from my birth; Thou hast been my God from my earliest breath!
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Oh, be not far from me, for trouble is near; For there is none to help!
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many bulls surround me; Strong bulls of Bashan close me in on every side.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They open their mouths wide against me, Like a ravening and roaring lion.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 I am poured out like water, And all my bones are out of joint; My heart is become like wax; It melteth in my bosom.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 My strength is dried up like an earthen vessel, And my tongue cleaveth to my jaws; Thou hast brought me to the dust of death!
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 For dogs have surrounded me; Bands of evil-doers have encompassed me, —Like lions my hands and my feet.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 I can count all my bones; They gaze, and feast their eyes upon me.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 They divide my garments among them, And for my vesture they cast lots.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 But be not thou far from me, O LORD! O my strength! make haste to mine aid!
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Deliver my life from the sword; My blood from the power of the dog;
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Save me from the lion's mouth; Shield me from the horns of the buffaloes!
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I will proclaim thy name to my brethren; In the midst of the congregation will I praise thee.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Praise him, ye worshippers of Jehovah! Extol him, all ye race of Jacob. And fear him, all ye race of Israel!
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 For he hath not despised nor abhorred the misery of the afflicted. Nor hath he hid his face from him; But when he cried unto him, he heard.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 My praise shall be of thee in the great congregation; I will pay my vows before them that fear him!
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 The afflicted shall eat, and be satisfied; They that seek the LORD shall praise him; Your hearts shall be glad for ever and ever!
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 All the ends of the earth shall remember, and turn to Jehovah; All the families of the nations shall worship before thee!
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 For the kingdom is Jehovah's; He is the governor of the nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All the rich of the earth shall eat and worship; Before him shall they also bow, who are going down to the dust, Who cannot keep themselves alive.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 The future generation shall serve him; The race which is to come shall hear of Jehovah.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 They shall come, and declare his righteousness; His mighty deeds to the people that shall be born.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psalms 22 >