< Psalms 20 >
1 “For the leader of the music. A psalm of David.” May Jehovah hear thee in the day of trouble; May the name of the God of Jacob defend thee!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
2 May he send thee help from his sanctuary, And strengthen thee out of Zion!
Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
3 May he have regard to all thine offerings, And accept thy burnt sacrifice! (Pause)
Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
4 May he grant thee thy heart's desire, And fulfill all thy purposes!
Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
5 We will rejoice in thy protection, And in the name of our God will we set up our banners, When Jehovah hath fulfilled all thy petitions.
Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
6 Now I know that Jehovah helpeth his anointed; That he heareth him from his holy heaven, And aideth him with the saving strength of his right hand.
Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
7 Some glory in chariots, and some in horses, But we in the name of Jehovah our God.
Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
8 They stumble and fall, But we stand and are erect.
Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
9 The LORD save the king! May he hear us when we call!
Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!