< Psalms 18 >

1 I love thee, O LORD, my strength!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Jehovah is my rock, my fortress, and my deliverer; My God, my strength, in whom I trust; My shield, my strong defence, and my high tower.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 I called upon the LORD, who is worthy to be praised, And was delivered from my enemies.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 The snares of death encompassed me; The floods of destruction filled me with dismay;
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 The snares of the underworld surrounded me, And the nets of death seized upon me. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 In my distress I called upon the LORD, And cried unto my God; He heard my voice from his palace, And my cry came before him into his ears.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Then the earth quaked and trembled; The foundations of the mountains rocked and were shaken, Because his wrath was kindled.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 A smoke went up from his nostrils, And fire from his mouth devoured; Burning coals shot forth from him.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 He bowed the heavens, and came down; And darkness was under his feet;
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 And he rode upon a cherub, and did fly; Yea, he did fly upon the wings of the wind.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 And he made darkness his covering; His pavilion round about him was dark waters and thick clouds of the skies.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 At the brightness before him, his thick clouds passed away; Then came hailstones and coals of fire.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 The LORD also thundered from heaven, And the Most High uttered his voice, Amid hailstones and coals of fire.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 He sent forth his arrows, and scattered them; Continual lightnings, and discomfited them.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Then the channels of the deep were seen, And the foundations of the earth were laid bare At thy rebuke, O LORD! At the blast of the breath of thy nostrils.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 He stretched forth his hand from above; he took me, And drew me out of deep waters.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 He delivered me from my strong enemy; From my adversaries, who were too powerful for me.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 They fell upon me in the day of my calamity; But the LORD was my stay.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 He brought me forth into a large place; He delivered me, because he delighted in me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 The LORD hath rewarded me according to my righteous; According to the cleanness of my hands hath he recompensed me.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For I have kept the ways of the LORD, And have not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 For all his laws were in my sight; I did not put away his statutes from me.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 I was upright before him, And kept myself from iniquity.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Therefore hath the LORD rewarded me according to my righteousness, According to the cleanness of my hands before his eyes.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 To the merciful thou showest thyself merciful; To the upright thou showest thyself upright;
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 To the pure thou showest thyself pure, And to the perverse thou showest thyself perverse.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For thou savest the afflicted people, But the haughty countenance thou bringest down.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 Thou causest my lamp to shine; Jehovah, my God, enlighteneth my darkness.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 For through thee I have broken through troops; Through my God I have leaped over walls.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 The ways of God are just and true; His word is pure, tried in the fire; He is a shield to all who put their trust in him.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Who, then, is God, save Jehovah? And who is a rock, save our God?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 It is God that girded me with strength, And made my way plain.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 He made my feet like the hind's, And set me in my high places;
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 He taught my hands to war, So that my arm bent the bow of brass.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Thou gavest me the shield of thy protection; Thy right hand held me up, And thy goodness made me great.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Thou didst make a wide path for my steps, So that my feet did not stumble.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 I pursued my enemies and overtook them, And turned not back till I had destroyed them.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 I smote them, so that they could not rise; They fell under my feet.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Thou didst gird me with strength for the battle; Thou didst cast down my adversaries under me.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 Thou didst cause my enemies to turn their backs, So that I destroyed them that hated me.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They cried, but there was none to help; To Jehovah, but he answered them not.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 I beat them small, like dust before the wind; I cast them out as the dirt of the streets.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Thou hast delivered me from the assaults of the nations; Thou hast made me the head of the kingdoms. Nations whom I knew not serve me;
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 They who have only heard of me obey me; Yea, men of a strange land submit themselves to me;
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Men of a strange land fade away, like a leaf, And come trembling from their strongholds.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Jehovah is the living God; blessed be my rock; Exalted be the God of my salvation!
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 It is God who hath given me vengeance, And subdued the nations under me;
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 He delivered me from my enemies; Yea, thou hast lifted me up above my adversaries; Thou hast saved me from the violent man!
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 Therefore I will give thanks to thee, O LORD! among the nations, And sing praises to thy name.
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Great deliverance giveth he to his king, And showeth mercy to his anointed, —To David and to his posterity for ever.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< Psalms 18 >