< Psalms 121 >
1 “A psalm of the steps, or the goings up.” I lift up mine eyes to the hills: Whence cometh my help?
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 My help cometh from the LORD, Who made heaven and earth.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 He will not suffer thy foot to stumble; Thy guardian doth not slumber.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 Behold, the guardian of Israel Doth neither slumber nor sleep.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 The LORD is thy guardian; The LORD is thy shade at thy right hand.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 The sun shall not smite thee by day, Nor the moon by night.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 The LORD will preserve thee from all evil; He will preserve thy life.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 The LORD will preserve thee, when thou goest out and when thou comest in, From this time forth for ever.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.