< Psalms 12 >
1 “For the leader of the music; to the octave. A psalm of David.” Help, LORD; for the godly man ceaseth; The faithful are failing among men.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 They speak falsehood one to another; With flattering lips, with a double heart, do they speak.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 May the LORD destroy all flattering lips, And the tongue which speaketh proud things!
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 Who say, “With our tongues will we prevail; Our lips are our reliance; Who is lord over us?”
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 For the oppression of the poor and the sighing of the wretched, Now will I stand up, saith the LORD; I will set in safety him whom they puff at.
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 The words of the LORD are pure; Like silver purified in a furnace on the earth, Seven times refined.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 Thou, O LORD! will watch over them; Thou wilt preserve them from this generation for ever.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 The wicked walk on every side, When the vilest of men are exalted.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.