< Psalms 106 >
1 Praise ye the LORD! O give thanks to the LORD, for he is good; For his mercy endureth for ever!
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Who can utter the mighty deeds of the LORD? Who can show forth all his praise?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Happy are they who have regard to justice, Who practise righteousness at all times!
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Remember me, O LORD! with the favor promised to thy people; O visit me with thy salvation!
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 That I may see the prosperity of thy chosen, That I may rejoice in the joy of thy people, That I may glory with thine inheritance!
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 We have sinned with our fathers; We have committed iniquity; we have done wickedly.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Our fathers in Egypt did not regard thy wonders; They remembered not the multitude of thy mercies; But rebelled at the sea, the Red sea.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Yet he saved them for his own name's sake. That he might make his mighty power to be known.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 He rebuked the Red sea, and it was dried up, And he led them through the deep as through a desert.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 He saved them from the hand of him that hated them, And redeemed them from the hand of the enemy.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 The waters covered their enemies; There was not one of them left.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Then believed they his words, And sang his praise.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 But they soon forgot his deeds, And waited not for his counsel.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 They gave way to appetite in the wilderness, And tempted God in the desert;
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 And he gave them their request, But sent upon them leanness.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 They also envied Moses in the camp, And Aaron, the holy one of the LORD.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Then the earth opened, and swallowed up Dathan, And covered the company of Abiram,
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 And a fire was kindled in their company; The flames burned up the wicked.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 They made a calf in Horeb, And worshipped a molten image;
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 They changed their God of glory Into the image of a grass-eating ox.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 They forgot God, their saviour, Who had done such great things in Egypt,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Such wonders in the land of Ham. Such terrible things at the Red sea.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Then he said that he would destroy them; Had not Moses, his chosen, stood before him in the breach, To turn away his wrath, that he might not destroy them.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 They also despised the pleasant land, And believed not his word;
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 But murmured in their tents, And would not hearken to the voice of the LORD.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Then he lifted up his hand against them, And swore that he would make them fall in the wilderness;
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 That he would overthrow their descendants among the nations, And scatter them in the lands.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 They also gave themselves to the worship of Baal-peor, And ate sacrifices offered to lifeless idols.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Thus they provoked his anger by their practices, And a plague broke in upon them.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Then stood up Phinehas, and executed judgment, And the plague was stayed.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 And this was counted to him for righteousness, To all generations for ever.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 They provoked him also at the waters of Meribah [[strife]], And evil befell Moses on their account.
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 For they provoked his spirit, So that he spake inconsiderately with his lips.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 They did not destroy the nations, As Jehovah had commanded them.
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 They mingled themselves with the peoples, And learned their practices.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 They even worshipped their idols, Which became to them a snare.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Their sons and their daughters they sacrificed to demons,
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 And shed innocent blood, The blood of their own sons and daughters, Whom they sacrificed to the idols of Canaan; And the land was polluted with blood.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Thus they defiled themselves with their works, And played the harlot with their practices.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Then burned the anger of the LORD against his people, So that he abhorred his own inheritance.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 And he gave them into the hand of the nations, And they who hated them ruled over them.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Their enemies oppressed them, And they were bowed down under their hand.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Many times did he deliver them; But they provoked him by their devices, And they were brought low for their iniquities.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Yet, when he heard their cries, He had regard to their affliction;
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 He remembered his covenant with them, And repented according to the greatness of his mercy,
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 And caused them to find pity Among all that carried them captive.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Save us, O Jehovah, our God! and gather us from among the nations, That we may give thanks to thy holy name, And glory in thy praise!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 [Blessed be Jehovah, the God of Israel, From everlasting to everlasting! And let all the people say, Amen! Praise ye Jehovah!]
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.