< Psalms 101 >
1 “A psalm of David.” I will sing of mercy and justice; To thee, O LORD! will I sing!
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
2 I will have regard to the way of uprightness: When thou shalt come to me, I will walk within my house with an upright heart.
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
3 I will set no wicked thing before mine eyes; I hate the work of evil-doers; It shall not cleave to me.
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
4 The perverse in heart shall be far from me; I will not know a wicked person.
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
5 Whoso slandereth his neighbor in secret, him will I cut off; Him that hath a haughty look and a proud heart I will not endure.
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
6 Mine eyes shall be upon the faithful of the land, that they may dwell with me; He that walketh in the way of uprightness shall serve me.
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
7 He who practiseth deceit shall not dwell in my house; He who telleth lies shall not remain in my sight.
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
8 Every morning will I destroy the wicked of the land, That I may cut off all evil-doers from the city of the LORD.
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.