< Proverbs 8 >
1 Doth not wisdom cry aloud, And understanding put forth her voice?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Upon the top of the high places, By the wayside, In the cross-ways, She taketh her station.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 By the side of the gates, In the entrance of the city, In the approaches to the doors, she crieth aloud.
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 “To you, O men! do I call, And my voice is to the sons of men!
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 O ye simple ones! learn wisdom, And ye fools, be ye of an understanding heart!
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Hear, for I speak excellent things, And my lips utter that which is right.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 For my mouth speaketh truth, And wickedness is an abomination to my lips.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 All the words of my mouth are in uprightness; There is nothing crooked or deceitful in them;
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 They are all plain to the man of understanding, And right to those who find knowledge.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Receive my instruction, and not silver. And knowledge rather than choice gold!
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 For wisdom is better than pearls, And no precious things are to be compared with her.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 “I, wisdom, dwell with prudence, And find out the knowledge of sagacious counsels.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 The fear of the LORD is to hate evil; Pride, and arrogance, and the evil way, And the deceitful mouth, do I hate.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Counsel is mine, and sound reason; I am understanding; I have strength.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 By me kings reign, And princes decree justice.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 By me princes rule, And nobles, even all the judges of the earth.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 I love them that love me, And they who seek me early shall find me.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Riches and honor are with me; Yea, durable riches and prosperity.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 My fruit is better than gold, yea, than fine gold. And my revenue than choice silver.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 I walk in the way of righteousness, In the midst of the paths of equity.
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 I cause those who love me to possess substance; Yea, I fill their treasuries.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 “The LORD created me, the firstling of his course, Before his works, of old;
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 I was anointed from everlasting, From the beginning, even before the earth was made.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 When as yet there were no deeps, I was brought forth. When there were no springs, abounding with water.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Before the mountains were settled, Yea, before the hills, I was brought forth;
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Ere yet he had made the land and the wastes, And the first of the clods of the earth.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 When he framed the heavens, I was there; When he drew a circle upon the face of the deep;
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 When he made firm the sky above, And the fountains of the deep rushed forth;
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 When he gave to the sea its bounds, that the waters should not pass their border; When he marked out the foundations of the earth, —
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Then was I by him as a master-builder; I was his delight day by day, Exulting before him at all times;
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Exulting in the habitable part of his earth, And my delight was with the sons of men.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 “Now, therefore, ye children, hearken to me! For happy are they who keep my ways!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Hear instruction, and be wise! Yea, reject it not!
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Happy the man who hearkeneth to me, Who watcheth day by day at my gates, Who waiteth at the posts of my doors;
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 For he that findeth me findeth life, And obtaineth favor from the LORD;
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 But he who misseth me doeth violence to himself; All they who hate me love death.”
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”