< Mark 5 >
1 And they came to the other side of the lake, into the country of the Gerasenes.
Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa.
2 And when he had come out of the boat, immediately there met him out of the tombs a man with an unclean spirit,
Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.
3 who had his dwelling in the tombs; and not even with a chain could any one bind him any longer;
Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari
4 because he had often been bound with fetters and chains, and the chains had been snapped asunder by him, and the fetters broken in pieces; and no one could master him;
An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.
5 and continually, night and day, in the tombs and in the mountains, he was crying out, and cutting himself, with stones.
Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi.
6 And seeing Jesus afar off, he ran and bowed down before him,
Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.
7 and cried out with a loud voice, and said, What have I to do with thee, Jesus, Son of the most high God? I adjure thee by God, do not torment me.
Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala,
8 For he was saying to him, Unclean spirit, come out from the man.
Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa.”
9 And he asked him, What is thy name? And he saith to him, Legion is my name; for we are many.
Ya tambaye shi, “Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa.
10 And he besought him much not to send them out of the country.
Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.
11 Now there was there, by the mountain, a great herd of swine feeding.
Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni.
12 And they besought him, saying, Send us into the swine, that we may enter into them.
Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun.
13 And he gave them leave. And the unclean spirits coming out, entered into the swine; and the herd rushed down the steep into the lake, about two thousand, and were drowned in the lake.
Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.
14 And they that fed them fled, and told the news in the city and in the country. And they came to see what had been done.
Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru
15 And they come to Jesus, and see him who had been possessed by demons, sitting, clothed, and in his right mind, —him who had had the legion; and they were afraid.
Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.
16 And they who saw it told them how it befell him that was possessed by the demons, and concerning the swine.
Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun.
17 And they began to beseech him to depart from their borders.
Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.
18 And when he was going on board the boat, he that had been possessed by the demons besought him that be might be with him.
Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi.
19 And he did not permit him, but said to him, Go to thy house to thy friends, and tell them how great things the Lord hath done for thee, and that he hath had compassion on thee.
Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka.
20 And he departed, and began to publish in Decapolis how great things Jesus had done for him; and all wondered.
Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.
21 And when Jesus had crossed again in the boat to the ether side, a great multitude gathered about him; and he was by the lake.
Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun.
22 And there cometh one of the rulers of the synagogue, Jairus by name; and seeing him, he fell at his feet,
Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa.
23 and besought him much, saying, My little daughter lieth at the point of death; I pray thee, come and lay thy hands on her, that she may be saved and live.
Ya yi ta rokonsa, yana cewa, “Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu.”
24 And he went with him; and a great multitude followed him, and pressed upon him.
Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.
25 And a woman, who had had an issue of blood twelve years,
Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu.
26 and had undergone much at the hands of many physicians, and spent all that she had, and was not at all benefited, but rather grew worse,
Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi.
27 having heard about Jesus, came in the crowd behind, and touched his garment.
Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.
28 For she said, If I touch even his garments, I shall be made well.
Domin ta ce “Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke.”
29 And immediately the fountain of her blood was dried up; and she perceived in her body that she was cured of her plague.
Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.
30 And Jesus immediately perceiving in himself that power had gone out from him, turned round in the crowed, and said, Who touched my garments?
Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce “wanene ya taba rigata?”
31 And his disciples said to him, Thou seest the multitude pressing on thee, and dost thou say, Who touched me?
Almajiransa suka ce, “a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?”
32 And he looked round to see her who had done this.
Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.
33 But the woman, fearing and trembling, knowing what had been done to her, came and fell down before him, and told him all the truth.
Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya.
34 And he said to her, Daughter, thy faith hath made thee well; go in peace, and be recovered from thy plague.
Sai ya ce da ita, “Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki”.
35 While he was yet speaking, there came from the house I of the ruler of the synagogue some who said, Thy daughter is dead; why dost thou trouble the Teacher any further?
Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce “Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?”
36 And Jesus, overhearing those words, saith to the ruler of the synagogue, Fear not; only believe.
Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, “kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai.”
37 And he suffered no one to follow him except Peter and James, and John the brother of James.
Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu.
38 And they come to the house of the ruler of the synagogue; and he seeth a tumult, and people weeping and wailing greatly.
Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.
39 And going in, he saith to them, Why do ye make this confusion and weeping? The child is not dead, but is sleeping.
Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane “Me ya sa kuke damuwa da kuka?” Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi.
40 And they laughed him to scorn. But putting them all out, he taketh the father of the child, and the mother, and those who were with him, and entereth where the child was.
Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.
41 And taking hold of the hand of the child, he saith to her, Talitha, kum; which is, when interpreted, Damsel, I say to thee, arise!
Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita “Tilatha koum” wato yarinya na ce ki tashi”
42 And immediately the damsel arose and walked; for she was twelve years old. And immediately they were greatly astonished.
Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya [gama shekarun ta sun kai goma sha biyu]. Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske.
43 And he charged them strictly that no one should know it, and bade that something should be given her to eat.
Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.