< Mark 3 >

1 And he entered again into a synagogue; and there was a man there having a withered hand;
Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu.
2 and they watched him, whether he would heal him on the sabbath, that they might accuse him.
Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.
3 And he saith to the man having the withered hand, Stand up in the midst.
Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun “Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa.”
4 And he saith to them, Is it lawful to do good on the sabbath, or to do evil? to save life, or to kill? But they were silent.
Sai ya ce wa mutane, “Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? “Amma suka yi shiru.
5 And looking round on them with anger, being grieved for the hardness of their hearts, he saith to the man, Stretch forth thy hand. And he stretched it forth; and his hand was restored.
Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi.
6 And the Pharisees went forth, and immediately had a consultation with the Herodians against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7 And Jesus withdrew with his disciples to the lake; and a great multitude from Galilee, and from Judaea followed;
Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya
8 and from Jerusalem, and from Idumaea, and from beyond the Jordan, and the people about Tyre and Sidon, a great multitude, when they heard what great things he was doing, came to him.
Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9 And he gave direction to his disciples, that a boat should be in readiness for him because of the multitude, that they might not throng him.
Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi.
10 For he had healed many, so that as many as had plagues pressed upon him to touch him.
Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11 And the unclean spirits, when they saw him, fell down before him, and cried out, saying, Thou art the Son of God.
Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne.”
12 And he strictly charged them that they should not make him known.
Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13 And he goeth up into the mountain, and calleth to him whom he would; and they came to him.
Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa.
14 And he appointed twelve to be with him, and whom he might send forth to preach,
Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi,
15 and to have authority to cast out demons. And he appointed the twelve,
Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu.
16 and Simon he surnamed Peter;
Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17 and James the son of Zebedee, and John the brother of James; and he surnamed them Boanerges, that is, Sons of thunder;
Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa,
18 and Andrew, and Philip, and Bartholomew, and Matthew, and Thomas, and James the son of Alphaeus, and Thaddaeus, and Simon of Cana,
da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye,
19 and Judas Iscariot, who betrayed him. And he cometh into the house.
da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20 And again a multitude cometh together, so that they could not so much as eat bread.
Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci,
21 And his relations hearing of it went out to lay hold of him; for they said, He is beside himself.
Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, “Ai, baya cikin hankalinsa “
22 And the scribes who came down from Jerusalem said, He hath Beelzebul; and, He casteth out the demons through the prince of the demons.
Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce “Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.”
23 And calling them to him, he said to them in parables: How can Satan cast out Satan?
Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, “Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan?
24 And if a kingdom be divided against itself, that kingdom cannot stand;
idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba.
25 and if a house be divided against itself, that house will not be able to stand;
Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26 and if Satan rise up against himself, he is divided, and cannot stand, but hath an end.
Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan.
27 Moreover, no one can enter into a strong man's house, and plunder his goods, unless he first bind the strong man; and then he will plunder his house.
Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28 Truly do I say to you, All sins will be forgiven the sons of men, and the blasphemies wherewith they shall blaspheme;
Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta,
29 but he that shall blaspheme against the Holy Spirit hath no forgiveness forever, but is exposed to everlasting sin.— (aiōn g165, aiōnios g166)
amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Because they said, He hath an unclean spirit.
“Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,”
31 And his mother and his brothers came; and, standing without, sent to him, to call him.
Sa'an nan uwatasa, da “Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo.
32 And a multitude was sitting about him; and they say to him, Lo! thy mother and thy brothers and thy sisters are without, seeking for thee.
Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka.”
33 And he answering saith to them, Who is my mother, and my brothers?
Ya amsa masu, “Dacewa su wanene uwa-ta da “yan'uwa na? “
34 And looking round on those who sat about him, he saith, Behold my mother and my brothers.
Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, “Ga uwa-ta da yan-uwana anan!
35 Whoever shall do the will of God, he is my brother, and sister, and mother.
Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta.”

< Mark 3 >