< Mark 3 >
1 And he entered again into a synagogue; and there was a man there having a withered hand;
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 and they watched him, whether he would heal him on the sabbath, that they might accuse him.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 And he saith to the man having the withered hand, Stand up in the midst.
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 And he saith to them, Is it lawful to do good on the sabbath, or to do evil? to save life, or to kill? But they were silent.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 And looking round on them with anger, being grieved for the hardness of their hearts, he saith to the man, Stretch forth thy hand. And he stretched it forth; and his hand was restored.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 And the Pharisees went forth, and immediately had a consultation with the Herodians against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 And Jesus withdrew with his disciples to the lake; and a great multitude from Galilee, and from Judaea followed;
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 and from Jerusalem, and from Idumaea, and from beyond the Jordan, and the people about Tyre and Sidon, a great multitude, when they heard what great things he was doing, came to him.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 And he gave direction to his disciples, that a boat should be in readiness for him because of the multitude, that they might not throng him.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 For he had healed many, so that as many as had plagues pressed upon him to touch him.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 And the unclean spirits, when they saw him, fell down before him, and cried out, saying, Thou art the Son of God.
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 And he strictly charged them that they should not make him known.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 And he goeth up into the mountain, and calleth to him whom he would; and they came to him.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 And he appointed twelve to be with him, and whom he might send forth to preach,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 and to have authority to cast out demons. And he appointed the twelve,
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 and Simon he surnamed Peter;
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 and James the son of Zebedee, and John the brother of James; and he surnamed them Boanerges, that is, Sons of thunder;
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 and Andrew, and Philip, and Bartholomew, and Matthew, and Thomas, and James the son of Alphaeus, and Thaddaeus, and Simon of Cana,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 and Judas Iscariot, who betrayed him. And he cometh into the house.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 And again a multitude cometh together, so that they could not so much as eat bread.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 And his relations hearing of it went out to lay hold of him; for they said, He is beside himself.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 And the scribes who came down from Jerusalem said, He hath Beelzebul; and, He casteth out the demons through the prince of the demons.
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 And calling them to him, he said to them in parables: How can Satan cast out Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 And if a kingdom be divided against itself, that kingdom cannot stand;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 and if a house be divided against itself, that house will not be able to stand;
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 and if Satan rise up against himself, he is divided, and cannot stand, but hath an end.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Moreover, no one can enter into a strong man's house, and plunder his goods, unless he first bind the strong man; and then he will plunder his house.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 Truly do I say to you, All sins will be forgiven the sons of men, and the blasphemies wherewith they shall blaspheme;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 but he that shall blaspheme against the Holy Spirit hath no forgiveness forever, but is exposed to everlasting sin.— (aiōn , aiōnios )
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn , aiōnios )
30 Because they said, He hath an unclean spirit.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 And his mother and his brothers came; and, standing without, sent to him, to call him.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 And a multitude was sitting about him; and they say to him, Lo! thy mother and thy brothers and thy sisters are without, seeking for thee.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 And he answering saith to them, Who is my mother, and my brothers?
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 And looking round on those who sat about him, he saith, Behold my mother and my brothers.
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Whoever shall do the will of God, he is my brother, and sister, and mother.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”