< Mark 14 >
1 And two days after was the passover, and the feast of unleavened bread; and the chief priests and the scribes sought how they might seize him by craft, and put him to death.
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 For they said, Not at the feast, lest there be an uproar among the people.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 And when he was at Bethany, in the house of Simon the leper, as he was reclining at table, there came a woman having an alabaster bottle of ointment of pure spikenard, very precious; and breaking the bottle, she poured it on his head.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 And there were some that were much displeased, [[and said]] among themselves, Why is this waste of the ointment made?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 For this ointment might have been sold for more than three hundred denaries, and given to the poor. And they chid her harshly.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 But Jesus said, Let her alone; why do ye trouble her? A good deed hath she done for me.
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 For the poor ye have always with you, and whenever ye will, ye can do good to them; but me ye have not always.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 She hath done what she could; she hath anointed my body beforehand for its burial.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 And truly do I say to you, Wherever the glad tidings shall be published throughout the whole world, this too which she hath done will be told for a memorial of her.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 And Judas Iscariot, one of the twelve, went to the chief priests, that he might deliver him up to them.
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 And they when they heard it were glad, and promised to give him money. And he sought a good opportunity to deliver him up.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 And on the first day of the feast of unleavened bread, when they used to kill the passover, his disciples say to him, Where wilt thou that we go and make ready for thee to eat the passover?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 And he sendeth forth two of his disciples, and saith to them, Go into the city, and there will meet you a man bearing a pitcher of water; follow him;
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 and wherever he goeth in, say to the master of the house, The Teacher saith, Where is my guest-chamber, where I may eat the passover with my disciples?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 And he will show you a large upper room furnished and prepared; and there make ready for us.
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 And the disciples went forth, and came into the city, and found as he had told them; and they made ready the passover.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 And when it was evening, he cometh with the twelve.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 And as they were reclining at table and eating, Jesus said, Truly do I say to you, that one of you will betray me, —one that is eating with me.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 They began to be sorrowful, and to say to him one by one, Is it I?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 And he said to them, It is one of the twelve, one that is dipping with me in the dish.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 For the Son of man indeed goeth away, as it hath been written concerning him; but woe to that man by whom the Son of man is betrayed! Well were it for that man if he had not been born.
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 And as they were eating, he took a loaf, and blessed, and broke it, and gave it to them, and said, Take; this is my body.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 And he took a cup, and having given thanks, gave it to them; and they all drank of it.
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 And he said to them, This is my blood of the covenant, which is shed for many.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 Truly do I say to you, I shall not drink hereafter of the fruit of the vine, until that day when I drink it new in the kingdom of God.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 And having sung a hymn, they went out to the Mount of Olives.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 And Jesus saith to them, Ye will all fall away from me; for it is written, “I will smite the shepherd, and the sheep will be scattered.”
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 But after I have risen, I will go before you into Galilee.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 But Peter said to him, Even if all shall fall away, yet will not I.
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 And Jesus saith to him, Truly do I say to thee, that even thou, to-day, on this night, before a cock crow twice, wilt thrice deny me.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 But he spoke the more vehemently: If I must die with thee, I will not deny thee. And so also said they all.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 And they come to a place called Gethsemane; and he saith to his disciples, Sit here, while I pray.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 And he taketh with him Peter and James and John; and began to be in great consternation and anguish.
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 And he saith to them, My soul is exceedingly sorrowful, even to death; remain here and watch.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 And going on a little farther, he fell on the ground, and prayed that, if it was possible, the hour might pass from him.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 And he said, Abba, Father, all things are possible to thee! take away this cup from me. But not what I will, but what thou wilt.
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 And he cometh and findeth them sleeping; and he saith to Peter, Simon, sleepest thou? Couldst not thou watch one hour?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Watch, and pray that ye enter not into temptation; the spirit indeed is willing, but the flesh is weak.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 And again he went away and prayed, saying the same words.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 And returning, he found them again sleeping, for their eyes were heavy; and they knew not what to answer him.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 And he cometh the third time, and saith to them, Sleep on, and take your rest! It is enough! the hour is come: lo! the Son of man is delivered up into the hands of sinners.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 Rise, let us be going; lo! he that delivereth me up is at hand.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 And immediately, while he was yet speaking, cometh Judas Iscariot, one of the twelve, and with him a multitude with swords and clubs, from the chief priests and the scribes and elders.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 And his betrayer had given them a signal, saying, Whomever I shall kiss, he is the man; seize him, and lead him away securely.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 And on coming he immediately went up to him, and said, Rabbi! and kissed him.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 And they laid hands on him and seized him.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 And one of those who stood by drew his sword, and smote the servant of the high-priest, and cut off his ear.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 And Jesus answering said to them, Ye have come out as against a robber, with swords and clubs, to take me.
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 I was daily with you in the temple, teaching, and ye did not lay hands on me; but [[thus it is]], that the Scriptures may be fulfilled.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 And all forsook him and fled.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 And there followed him a certain young man having a linen cloth wrapped round his naked body; and they laid hold of him.
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 And he left the linen cloth behind, and fled naked.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 And they led Jesus away to the high-priest; and all the chief priests and the elders and the scribes come together.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 And Peter followed him afar off, even into the court of the palace of the high-priest, and was sitting with the officers, and warming himself at the fire.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 And the chief priests and the whole council sought for testimony against Jesus in order to put him to death; and they found none.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 For many bore false witness against him, but their testimonies did not agree together.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 And some stood up and bore false witness against him, saying,
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 We heard him say, I will destroy this temple that is made with hands, and in three days I will build another not made with hands.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 And not even so did their testimony agree.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 And the high-priest stood up in the midst, and asked Jesus, saying, Dost thou make no answer to what these men testify against thee?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 But he was silent, and answered nothing. Again the high-priest asked him, and saith to him, Art thou the Christ, the Son of the Blessed?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 And Jesus said, I am; and ye will see the Son of man sitting on the right hand of Power, and coming with the clouds of heaven.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Then the high-priest rent his garments, and said, What further need have we of witnesses?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Ye have heard the blasphemy; what think ye? And they all condemned him as deserving the punishment of death.
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 And some began to spit on him, and to cover his face and buffet him, and say to him, Prophesy! And the officers, with blows, took him in charge.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 And as Peter was below in the court, there cometh one of the maid-servants of the high-priest;
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 and seeing Peter warming himself, she looked at him and said, Thou too wast with the Nazarene, Jesus.
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 But he denied, saying, I do not know nor understand what thou sayest. And he went out into the fore-court; and a cock crew.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 And the maid-servant, seeing him, began again to say to those who were standing by, This is one of them.
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 And he denied it again. And shortly after, those who were standing by said again to Peter, Surely thou art one of them; for thou art a Galilaean.
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 But he began to curse and to swear, saying, I know not this man of whom ye speak.
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 And immediately a cock crew a second time. And Peter called to mind the word that Jesus had said to him, Before a cock crows twice, thou wilt thrice deny me. And when he thought thereon, he wept.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.