< Mark 13 >
1 And as he went out of the temple, one of his disciples saith to him, Teacher, see! what stones, and what buildings!
Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
2 And Jesus said to him, Seest thou these great buildings? There will not be left one stone upon another, that will not be thrown down.
Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
3 And as he was sitting on the Mount of Olives, over against the temple, Peter and James and John and Andrew asked him privately,
Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
4 Tell us, when will these things be? and what will be the sign when all these things are about to be accomplished?
“Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
5 And Jesus began to say to them, See that no one deceive you.
Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
6 Many will come in my name, saying, I am He; and will deceive many.
Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
7 And when ye hear of wars, and rumors of wars, be not troubled; they must come to pass; but not yet is the end.
Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
8 For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom; there will be earthquakes in divers places; there will be famines. These things are the beginning of travail-pains.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
9 But do ye take heed to yourselves; they will deliver you up to councils, and ye will be taken into synagogues and beaten; and ye will be brought before governors and kings for my sake, for a testimony to them.
“Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
10 And the glad tidings must first be published to all the nations.
Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
11 And when they lead you away to deliver you up, be not anxious beforehand as to what ye shall speak; but whatever shall be given you in that hour, that speak; for it is not ye that speak, but the Holy Spirit.
Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
12 And brother will deliver up brother to death, and the father his child; and children will rise up against parents, and put them to death.
“Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
13 And ye will be hated by all on account of my name. But he that endureth to the end will be saved.
Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 But when ye see the abomination of desolation standing where it ought not, —let him that readeth understand, —then let those who are in Judaea flee to the mountains;
“Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
15 let not him that is on the house-top go down, nor enter, to take anything out of his house;
Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
16 and let not him that is in the field turn back to take his garment.
Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
17 And woe to the women with child, and to those with children at the breast, in those days!
Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
18 And pray that it may not be in winter.
Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
19 For those days will be a time of distress, such as hath not been from the beginning of the creation which God created until now, nor shall be.
Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
20 And if the Lord had not shortened the days, no flesh would have been saved; but for the sake of the chosen whom he chose, he shortened the days.
“Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
21 And then if any one shall say to you, See! here is the Christ; see! there; believe him not.
A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
22 For false Christs and false prophets will rise up, and will do signs and wonders, to lead astray, if possible, the chosen.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
23 But do ye take heed! I have told you all beforehand.
Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
24 But in those days, after that distress, the sun will be darkened, and the moon will not give her light;
“Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
25 and the stars will be falling from heaven, and the powers that are in the heavens will be shaken.
taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
26 And then will they see the Son of man coming in the clouds with great power and glory.
“Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
27 And then will he send forth the angels, and will gather the chosen ones from the four winds, from the uttermost part of the earth to the uttermost part of heaven.
Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
28 And from the fig-tree learn its parable. When its branch hath now become tender, and putteth forth its leaves, ye know that summer is near.
“To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
29 So also, when ye see these things coming to pass, know ye that he is near, at the doors.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
30 Truly do I say to you, that this generation will not pass away, till all these things take place.
Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
31 Heaven and earth will pass away, but my words will not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
32 But that day or hour knoweth no one, not even the angels in heaven, nor the Son, but the Father.
“Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
33 Take heed, watch; for ye know not when the time is.
Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
34 As a man going abroad, having left his house and given authority to his servants, to each one his work, also commanded the porter to watch,
Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
35 so also watch ye; for ye know not when the master of the house is coming, whether at evening, or at midnight, or at the cock-crowing, or in the morning;
“Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
36 lest coming suddenly, he find you sleeping.
In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
37 And what I say to you, I say to all: Watch.
Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”