< Mark 11 >

1 And when they were drawing near to Jerusalem and to Bethany, at the Mount of Olives, he sendeth forth two of his disciples,
Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu
2 and saith to them, Go to the village over against you; and immediately on entering it ye will find a colt tied, on which no man hath yet sat; loose and bring it.
ya ce masu, “ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani.
3 And if any one say to you, Why do ye this? say, The Lord hath need of it, and will immediately send it back hither.
In wani ya ce maku, “Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan.”'
4 And they went, and found the colt tied by the door without, on the street; and they loose it.
Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.
5 And some of those who were standing there said to them, What are ye about, loosing the colt?
sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, “Don me kuke kwance aholakin nan?
6 And they said to them as Jesus had commanded; and they let them go.
Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.
7 And they bring the colt to Jesus, and put their garments on it; and he sat upon it.
Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau.
8 And many spread their garments on the road; and others boughs, having cut them from the fields.
Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen.
9 And they that went before, and they that followed, cried, Hosanna! Blessed is he that cometh in the name of the Lord!
Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.
10 Blessed is the coming kingdom of our father David! Hosanna in the highest heavens!
Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!”
11 And he entered Jerusalem, and the temple; and having looked round on all things, the evening being now come, he went out to Bethany, with the twelve.
San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan.
12 And on the morrow, when they had come from Bethany, he was hungry;
Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.
13 and seeing a fig-tree afar off having leaves, he went to see whether he might find anything on it; and on coming to it he found nothing but leaves; for the season of figs had not come.
Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.
14 And he answering said to it, Let no one eat fruit from thee henceforth for ever. And his disciples heard him. (aiōn g165)
Sai ya ce wa bauren, “Kada kowa ya kara cin ''ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa sun ji maganar. (aiōn g165)
15 And they come to Jerusalem. And he went into the temple, and began to cast out those who sold and bought in the temple, and overturned the tables of the money-changers, and the seats of those who sold the doves;
Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru.
16 and he suffered no one to carry any vessel through the temple.
Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.
17 And he taught, and said to them, Is it not written, “My house shall be called a house of prayer for all the nations? but ye have made it a den of robbers.”
Sai ya koyar da su cewa, “Ashe ba rubuce yake ba, “Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi”.
18 And the chief priests and the scribes heard it, and sought how they might destroy him; for they feared him; because all the multitude was astonished at his teaching.
Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa.
19 And when it became late, he went out of the city.
Kowace yamma kuma, sukan fita gari.
20 And in the morning, as they were passing by, they saw the fig-tree withered from the roots.
Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe.
21 And Peter remembered and said to him, Rabbi, see! the fig-tree which thou didst curse is withered away.
Bitrus kuwa ya tuna ya ce “Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe.”
22 And Jesus answering saith to them, Have faith in God.
Yesu ya amsa masu ya ce, “ku gaskata da Allah.”
23 Truly do I say to you, that whoever shall say to this mountain, Be thou taken up, and cast into the sea, and shall not doubt in his heart, but shall believe that what he saith will come to pass, he shall have it.
Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.
24 Therefore I say to you, All things whatever ye pray for and ask, believe that ye have obtained, and ye shall have them.
Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku.
25 And when ye stand praying, forgive, if ye have aught against any one, that your Father who is in heaven may also forgive you your trespasses.
Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi.”
(Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)
27 And they come again to Jerusalem. And as he was walking in the temple, there come to him the chief priests and the scribes and the elders;
Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa,
28 and they said to him, By what authority doest thou these things? or who gave thee this authority to do these things?
suka ce masa, “Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu? “
29 And Jesus said to them, I will ask you one question; and answer me, and I will tell you by what authority I do these things.
Sai Yesu ya ce masu, “Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan.
30 The baptism of John, was it from heaven, or from men? Answer me.
Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa”.
31 And they reasoned among themselves, saying, If we say, From heaven, he will say, Why then did ye not believe him?
Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, “in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, “To, don me ba ku gaskata shi ba?
32 But shall we say, From men? They feared the people; for all regarded John as truly a prophet.
In kuwa muka ce, “amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.
33 And they answered and said to Jesus, We do not know. And Jesus saith to them, Neither do I tell you by what authority I do these things.
Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba” Yesu ya ce masu, “Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba.”

< Mark 11 >