< Luke 4 >

1 And Jesus, full of the Holy Spirit, returned from the Jordan, and was led in the Spirit in the wilderness
Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
2 forty days, tempted by the Devil. And he ate nothing in those days; and when they were ended, he was hungry.
inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
3 And the Devil said to him, If thou art the Son of God, command this stone that it become a loaf of bread.
Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
4 And Jesus answered him, It is written, “Not on bread alone shall man live.”
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
5 And taking him up, he showed him all the kingdoms of the world in a moment of time.
Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
6 And the Devil said to him, All this power will I give thee, and their glory; because to me it hath been delivered, and I give it to whomever I will.
Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
7 If thou then wilt worship me, it shall all be thine.
Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
8 And Jesus answering said to him, It is written, “Thou shalt worship the Lord thy God, and him only shalt thou serve.”
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
9 And he brought him to Jerusalem, and set him on the pinnacle of the temple, and said to him, If thou art the Son of God, cast thyself down from hence;
Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
10 for it is written, “He will give his angels charge concerning thee, to guard thee;
Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
11 and in their hands they will bear thee up, that thou mayst not dash thy foot against a stone.”
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
12 And Jesus answering said to him, It hath been said, “Thou shalt not make trial of the Lord thy God.”
Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
13 And when he had brought every temptation to an end, the Devil departed from him for a season.
Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
14 And Jesus returned in the power of the Spirit into Galilee; and there went out a report concerning him through all the surrounding country
Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
15 And he taught in their synagogues, honored by all.
Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
16 And he came to Nazara, where he had been brought up, and, as his custom was, he went into the synagogue on the sabbath-day; and stood up to read.
Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
17 And there was delivered to him the book of the prophet Isaiah; and unrolling the book, he found the place where it was written,
Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
18 “The Spirit of the Lord is upon me, because he anointed me to preach glad tidings to the poor; he hath sent me to proclaim deliverance to the captives, and recovering of sight to the blind, to set at liberty the oppressed,
“Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
19 to proclaim the acceptable year of the Lord.”
In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
20 And rolling up the book, he gave it back to the attendant, and sat down; and the eyes of all in the synagogue were fixed upon him.
Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
21 And he began to say to them, To-day hath this scripture been fulfilled in your ears.
Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
22 And they all spoke in his praise, and wondered at the words of grace which proceeded from his mouth; and they said, Is not this Joseph's son?
Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
23 And he said to them, Ye will doubtless say to me this proverb, “Physician, heal thyself;” whatever things we have heard of as having been done in Capernaum, do here too in thy own country.
Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
24 And he said, Truly do I say to you, No prophet is acceptable in his own country.
Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
25 But I tell you in truth, that there were many widows in Israel in the days of Elijah, when the heaven was shut up three years and six months, and there was a great famine throughout all the land;
Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
26 and yet to none of them was Elijah sent, but to Sarepta in Sidonia, to a woman that was a widow.
Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
27 And there were many lepers in Israel in the time of Elisha the prophet; and not one of them was cleansed, but only Naaman the Syrian.
Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
28 And all in the synagogue, when they heard this, were filled with wrath.
Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
29 And they rose up, and forced him out of the city and took him to the brow of the hill on which their city was built, to cast him down headlong;
Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
30 but he, passing through the midst of them, went away.
amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
31 And he came down to Capernaum, a city of Galilee, and was teaching them on the sabbath.
Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
32 And they were astonished at his teaching; for his word was with authority.
Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
33 And in the synagogue there was a man having a spirit of an unclean demon, and he cried out with a loud voice,
A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
34 Ha! what have we to do with thee, Jesus of Nazareth? Thou hast come to destroy us. I know who thou art, the Holy One of God.
“Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
35 And Jesus rebuked him, saying, Be silent, and come out of him. And the demon threw him down in the midst, and came out of him, having done him no hurt.
Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
36 And all were amazed; and they spoke with one another, saying, What kind of word is this, that with authority and power he commandeth the unclean spirits, and they come out?
Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
37 And there went out a report concerning him into every place of the surrounding country.
Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
38 And he arose and went from the synagogue into the house of Simon. And Simon's wife's mother was seized with a great fever; and they besought him for her.
Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
39 And standing over her, he rebuked the fever, and it left her. And immediately she arose and waited on them.
Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
40 And when the sun was setting, all who had any sick with divers diseases brought them to him; and he laid his hands on every one of them, and healed them.
Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
41 And demons also came out from many, crying out, and saying, Thou art the Son of God. And he rebuked them, and did not suffer them to speak, because they knew that he was the Christ.
Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
42 And when it was day, he went out, and betook himself to a desert place; and the multitudes went in search of him; and they came to him, and would have prevented him from leaving them.
Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
43 But he said to them, I must publish the good tidings of the kingdom of God to the other cities also; because for this I was sent forth.
Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
44 And he continued to preach in the synagogues of Galilee.
Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.

< Luke 4 >