< Luke 3 >
1 Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Judaea, and Herod tetrarch of Galilee, and his brother Philip tetrarch of Ituraea and of the region of Trachonitis, and Lysanias tetrarch of Abilene,
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 when Annas and Caiaphas were high-priests, the word of God came to John, the son of Zachariah, in the wilderness.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 And he came into all the country about the Jordan, preaching the baptism of repentance for the remission of sins;
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 as it is written in the book of the words of Isaiah the prophet: “The voice of one crying in the wilderness, Prepare the way of the Lord, make straight his paths!
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Every valley shall be filled, and every mountain and hill shall be made low; and the crooked places shall be made straight, and the rough ways smooth;
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 and all flesh shall see the salvation of God.”
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 He said therefore to the multitudes that came forth to be baptized by him, Brood of vipers, who warned you to flee from the coming wrath?
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Bring forth therefore fruits worthy of repentance; and begin not to say within yourselves, We have Abraham for our father; for I say to you, that God is able out of these stones to raise up children to Abraham.
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 And already also is the axe lying at the root of the trees; every tree therefore that beareth not good fruit is to be cut down, and cast into the fire.
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 And the multitudes asked him, saying, What then must we do?
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 He answered and said to them, He that hath two coats, let him impart to him that hath none; and he that hath food, let him do likewise.
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 And there came also publicans to be baptized, and said to him, Teacher, what must we do?
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 And he said to them, Exact no more than hath been ordered you.
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 And soldiers also asked him, saying, And what must we do? And he said to them, Do violence to no one, accuse no one falsely, and be content with your wages.
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 And while the people were in expectation, and all were considering in their hearts concerning John, whether he were the Christ,
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 John answered and said to them all, I indeed baptize you with water; but he who is mightier than I is coming, the latchet of whose sandals I am not worthy to loose; he will baptize you in the Holy Spirit and in fire.
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 His winnowing-shovel is in his hand to thoroughly cleanse his threshing-floor, and gather the wheat into his garner; but the chaff he will burn up with unquenchable fire.
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 And giving many other exhortations he published the glad tidings to the people.
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 But Herod the tetrarch, being reproved by him on account of Herodias the wife of his brother, and on account of all the evil deeds which Herod had done,
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 added this also to them all, that he shut up John in prison.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 And it came to pass, when all the people had been baptized, and Jesus also had been baptized, and was praying, that the heaven was opened,
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 and the Holy Spirit descended upon him in a bodily shape as a dove; and a voice came from heaven: “Thou art my beloved Son; with thee I am well pleased.”
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 And Jesus himself was, when he began, about thirty years of age, being, as was supposed, the son of Joseph, who was the son of Heli,
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 who was the son of Matthath, who was the son of Levi, who was the son of Melchi, who was the son of Jannai, who was the son of Joseph,
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 who was the son of Mattathias, who was the son of Amos, who was the son of Nahum, who was the son of Esli, who was the son of Naggai,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 who was the son of Maath, who was the son of Mattathias, who was the son of Shimei, who was the son of Josech, who was the son of Joda,
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 who was the son of Joanan, who was the son of Rhesa, who was the son of Zerubbabel, who was the son of Shealtiel, who was the son of Neri,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 who was the son of Melchi, who was the son of Addi, who was the son of Kosam, who was the son of Elmadam, who was the son of Er,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 who was the son of Jesus, who was the son of Eliezer, who was the son of Jorim, who was the son of Matthath, who was the son of Levi,
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 who was the son of Simeon, who was the son of Judah, who was the son of Joseph, who was the son of Jonam, who was the son of Eliakim,
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 who was the son of Melea, who was the son of Menna, who was the son of Mattatha, who was the son of Nathan, who was the son of David,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 who was the son of Jesse, who was the son of Obed, who was the son of Boaz, who was the son of Salma, who was the son of Nahshon,
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 who was the son of Amminadab, who was the son of Admin, who was the son of Arni, who was the son of Hezron, who was the son of Pharez, who was the son of Judah,
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 who was the son of Jacob, who was the son of Isaac, who was the son of Abraham, who was the son of Terah, who was the son of Nahor,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 who was the son of Serug, who was the son of Reu, who was the son of Peleg, who was the son of Eber, who was the son of Shelah,
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 who was the son of Cainan, who was the son of Arphaxad, who was the son of Shem, who was the son of Noah, who was the son of Lamech,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 who was the son of Methuselah, who was the son of Enoch, who was the son of Jared, who was the son of Mahalaleel, who was the son of Cainan,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 who was the son of Enos, who was the son of Seth, who was the son of Adam, who was the son of God.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.