< John 7 >
1 After these things Jesus walked in Galilee; for he would not walk in Judaea, because the Jews sought to kill him.
Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
2 Now the feast of the Jews, the feast of tabernacles, was at hand.
To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
3 His brothers therefore said to him, Depart hence, and go into Judaea, that thy disciples also may see thy works which thou art doing.
Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
4 For no one doeth anything in secret, and yet himself seeketh to be known openly. If thou doest these things, manifest thyself to the world.
Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5 For even his brothers did not believe in him.
Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
6 Jesus saith to them, My time is not yet come; but your time is always ready.
Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
7 The world cannot hate you; but me it hateth, because I testify of it, that its works are evil.
Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8 Go ye up to the feast; I go not up to this feast; for my time is not yet fully come.
Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
9 Having said these things, he remained in Galilee.
Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10 But when his brothers had gone up to the feast, then he also went up, not openly, but as it were in secret.
Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
11 The Jews therefore sought him at the feast, and said, Where is that man?
Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
12 And there was much debating among the multitude concerning him. Some said, He is a good man; others said, Nay, but he deceiveth the multitude.
Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
13 No one, however, spoke openly of him, for fear of the Jews.
Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14 But when it was now the midst of the feast, Jesus went up into the temple and taught.
Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
15 The Jews therefore marveled, saying, How knoweth this man letters, having never learned?
Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
16 Jesus therefore answered them, and said, My teaching is not mine, but his that sent me.
Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 If any one is desirous to do his will, he will know concerning the teaching, whether it is from God, or whether I speak from myself.
Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 He that speaketh from himself seeketh his own glory; but he that seeketh the glory of him that sent him, he is true, and in him is no unrighteousness.
Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 Hath not Moses given you the Law? and none of you keepeth the Law! Why do ye seek to kill me?
Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 The multitude answered, Thou hast a demon! Who seeketh to kill thee?
Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
21 Jesus answered and said to them, I have done one good work, and ye are all wondering.
Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
22 Moses hath given you circumcision, (not that it is from Moses, but from the fathers; ) and ye on the sabbath circumcise a man.
Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23 If a man receive circumcision on the sabbath, that the law of Moses may not be broken, are ye angry at me, because I have restored soundness to the whole body of a man on the sabbath?
Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24 Judge not according to the appearance, but judge righteous judgment.
Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25 Then some of the men of Jerusalem said, Is not this he whom they seek to kill?
Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26 and see! he speaketh boldly, and they say nothing to him. Have the rulers discovered certainly that this man is the Christ?
Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27 Still, as to this man, we know whence he is; but when the Christ cometh, no one knoweth whence he is.
da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28 Jesus therefore cried aloud, teaching in the temple and saying, Ye both know me, and ye know whence I am; and I have not come of myself, but there is in truth one who sent me, whom ye know not.
Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29 I know him, because I am from him, and he hath sent me.
Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30 Therefore they sought to take him; but no one laid hands on him, because his hour had not yet come.
Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
31 But of the multitude many believed in him, and said, When the Christ cometh, will he do more signs than these which this man doeth?
Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
32 The Pharisees heard the multitude thus debating concerning him; and the chief priest and the Pharisees sent officers to seize him.
Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33 Jesus therefore said, Yet a little while I am with you, and then I go to him that sent me.
Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
34 Ye will seek me and not find me; and where I am, ye cannot come.
Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
35 The Jews therefore said among themselves, Whither will this man go, that we shall not find him? Will he go to the dispersed among the Greeks, and teach the Greeks?
Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
36 What meaneth this which he said, Ye will seek me, and not find me; and where I am, ye cannot come?
Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
37 On the last day, which is the great day, of the feast, Jesus stood and cried aloud, saying, If any one thirst, let him come to me, and drink.
To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
38 He that believeth in me, from within him, as the Scripture hath said, will flow rivers of living water.
Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
39 But this he said of the Spirit, which those that believed in him were to receive; for the Spirit was not yet, because Jesus was not yet glorified.
Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40 Some of the multitude therefore, when they heard these words, said, This is in truth the prophet. Others said, This is the Christ.
Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 Others said, Doth the Christ then come from Galilee?
Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
42 Hath not the Scripture said, that the Christ cometh from the seed of David, and from Bethlehem, the town where David was?
Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 So there was a division among the multitude because of him.
Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 And some of them wished to seize him; but no one laid hands on him.
Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 The officers therefore came to the chief priests and Pharisees, who said to them, Why did ye not bring him?
Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 The officers answered, Never man spoke like this man.
Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 The Pharisees answered them, Have ye also been deceived?
Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 Hath any one of the rulers believed in him? or of the Pharisees?
Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 but this multitude that know not the Law are accursed.
Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 Nicodemus saith to them, being one of them,
Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 Doth our law judge a man, unless it first hear from him, and know what he doeth?
“Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
52 They answered and said to him, Art thou too from Galilee? Search and see that no prophet ariseth from Galilee.
Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
53 (Joh 7:53 - 8:12: This passage is omitted as ungenuine by Tischendorf and most critical editors of the Greek Testament. It is found in some manuscripts, but not in the most ancient. It is, however, very generally regarded as a genuine relic of the teaching of Christ, though not forming a part of the fourth Gospel. I give it in the text of Tregelles, omitting the words which he incloses in brackets. Tregelles, however, does not suppose it to be genuine.) [[And they went each to his house;
Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.