< John 6 >

1 After these things Jesus went away across the lake of Galilee, that of Tiberias.
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 And a great multitude followed him, because they saw the signs which he wrought on the diseased.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 And Jesus went up into the mountain, and sat there with his disciples.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 And the passover, the feast of the Jews, was near.
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Jesus then lifting up his eyes, and seeing that a great crowd was coming to him, saith to Philip, Whence are we to buy bread, that these may eat?
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 But this he said to try him; for he himself knew what he was going to do.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Philip answered him, Two hundred denaries' worth of bread is not sufficient for them, that each one may take a tittle.
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 One of his disciples, Andrew, Simon Peter's brother, saith to him,
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 There is a lad here, who hath five barley-loaves, and two small fishes; but what are they among so many?
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 Jesus said, Make the men lie down. Now there was much grass in the place. So the men lay down, in number about five thousand.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Jesus then took the loaves, and having given thanks, distributed to those that were lying down; in like manner also of the fishes, as much as they desired.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 And when they were filled, he saith to his disciples, Gather up the fragments that remain over, that nothing may be lost.
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 So they gathered them up, and filled twelve baskets with the fragments of the five barley-loaves, which remained over and above to those that had eaten.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 The men therefore seeing the sign which he wrought, said, This is truly the prophet that was to come into the world.
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 Jesus therefore, knowing that they were about to come and take him by force to make him a king, withdrew again to the mountain alone.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 But when evening came, his disciples went down to the lake,
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 and having gone on board a boat, were going over the lake to Capernaum. And darkness had overtaken them, and Jesus had not yet come to them.
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 And as a strong wind was blowing, the waves ran high.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 When therefore they had rowed about twenty-five or thirty furlongs, they saw Jesus walking on the lake, and drawing near the boat; and they were afraid.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 But he saith to them, It is I, be not afraid.
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Then they were willing to receive him into the boat; and immediately the boat was at the land whither they were going.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 The day following, the multitude which stood on the other side of the lake having seen that there was no other boat there but one, and that Jesus did not go with his disciples into the boat, but that his disciples went away alone,
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 (but there came other boats from Tiberias near the place where they ate the bread, when the Lord had given thanks; )
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 when therefore the multitude saw that Jesus was not there nor his disciples, they went on board the boats, and came to Capernaum, seeking Jesus.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 And having found him on the other side of the lake, they said to him, Rabbi, when didst thou come hither?
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jesus answered them and said, Truly, truly do I say to you, Ye seek me, not because ye saw signs, but because ye ate of the loaves, and were filled.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Labor not for the food that perisheth, but for the food that endureth to everlasting life, which the Son of man giveth to you; for on him hath the Father set his seal, even God. (aiōnios g166)
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios g166)
28 Then they said to him, What are we to do, that we may work the works of God?
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Jesus answered and said to them, This is the work of God, that ye believe in him whom he sent.
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 They said therefore to him, What sign doest thou, that we may see, and believe thee? What dost thou work?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Our fathers ate the manna in the wilderness, as it is written, “He gave them bread from heaven to eat.”
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Jesus therefore said to them, Truly, truly do I say to you, Moses hath not given you the bread from heaven; but my Father is giving you the true bread from heaven.
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 For the bread of God is that which is coming down from heaven, and giving life to the world.
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 They said therefore to him, Lord, evermore give us this bread.
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Jesus therefore said to them, I am the bread of life; he that cometh to me will not hunger; and he that believeth in me will never thirst.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 But I said to you, that ye have even seen, and do not believe.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 All that the Father giveth me will come to me; and him that cometh to me I will in no wise cast out;
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 for I have come down from heaven, not to do my own will, but the will of him that sent me.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 And this is the will of him that sent me, that of all which he hath given me I should lose nothing, but should raise it up in the last day.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 For this is the will of my Father, that every one who looketh on the Son and believeth in him, shall have everlasting life; and I will raise him up in the last day. (aiōnios g166)
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios g166)
41 The Jews therefore murmured about him, because he said, I am the bread which came down from heaven;
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 and they said, Is not this Jesus, the son of Joseph, one whose father and mother we know? How is it then that this man saith, I have come down from heaven?
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Jesus therefore answered and said to them, Murmur not among yourselves.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 No one can come to me, unless the Father, who sent me, draw him: and I will raise him up in the last day.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 It is written in the prophets, “And they shall all be taught of God.” Every one that hath heard the Father, and hath learnt from him, cometh to me.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 Not that any one hath seen the Father, but he who is from God; he hath seen the Father.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 Truly, truly do I say to you, He that believeth hath everlasting life. (aiōnios g166)
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios g166)
48 I am the bread of life.
Ni ne burodin rai.
49 Your fathers ate the manna in the wilderness, and died.
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 This is the bread which is coming down from heaven, that one may eat of it and not die.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 I am the living bread which came down from heaven; if any one eat of my bread, he will live for ever. Yea, and the bread which I will give for the life of the world is my flesh. (aiōn g165)
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn g165)
52 The Jews therefore contended with one another, saying, How can this man give us his flesh to eat?
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Jesus therefore said to them, Truly, truly do I say to you, Unless ye eat the flesh of the Son of man and drink his blood, ye have no life in you.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 He that eateth my flesh and drinketh my blood hath everlasting life; and I will raise him up in the last day. (aiōnios g166)
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios g166)
55 For my flesh is true food, and my blood is true drink.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 He that eateth my flesh and drinketh my blood dwelleth in me, and I in him.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 As the living Father sent me, and I live by reason of the Father; so he that eateth me, he also shall live by reason of me.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 This is the bread which came down from heaven; not as the fathers ate, and died; he that eateth this bread will live for ever. (aiōn g165)
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 These things he said in a synagogue, while teaching in Capernaum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Many therefore of his disciples, when they heard this, said, This teaching is hard; who can listen to it?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 Jesus therefore knew within himself that his disciples were murmuring about this, and said to them, Doth this offend you?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 What then if ye behold the Son of man ascending where he was before?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 It is the spirit which maketh alive; the flesh profiteth nothing. The words which I have spoken to you are spirit, and are life.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 But there are some of you who do not believe. For Jesus knew from the beginning who they were that did not believe, and who it was that would betray him.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 And he said, For this cause I have told you, that no one can come to me, unless it hath been given him from the Father.
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 From this time many of his disciples went back, and walked no more with him.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Jesus therefore said to the twelve, Do ye also wish to go away?
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simon Peter answered him, Lord, to whom shall we go? Thou hast words of everlasting life; (aiōnios g166)
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios g166)
69 and we have believed and known, that thou art the Holy One of God.
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Jesus answered them, Did not I choose you twelve? and one of you is a devil!
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 He spoke of Judas, the son of Simon Iscariot; for it was he that was about to betray him, being one of the twelve.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)

< John 6 >