< John 4 >

1 When therefore Jesus knew that the Pharisees had heard that Jesus made and baptized more disciples than John,
Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
2 (though Jesus himself did not baptize, but his disciples, )
ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
3 he left Judaea, and went again to Galilee.
Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
4 And he must necessarily pass through Samaria.
To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
5 He cometh therefore to a city of Samaria, called Sychar, near the piece of land which Jacob gave to his son Joseph.
Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
6 And Jacob's well was there. Jesus therefore, being wearied with the journey, was sitting thus by the well. It was about the sixth hour.
Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
7 There cometh a woman of Samaria to draw water. Jesus saith to her, Give me to drink.
Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
8 For his disciples had gone away into the city to buy food.
(Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
9 The Samaritan woman saith to him, How is it that thou, who art a Jew, askest drink of me, who am a Samaritan woman? For Jews have no dealings with Samaritans.
Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
10 Jesus answered and said to her, If thou hadst known the gift of God, and who it is that saith to thee, Give me to drink, thou wouldst have asked of him, and he would have given thee living water.
Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
11 The woman saith to him, Sir, thou hast nothing to draw with, and the well is deep. Whence hast thou the living water?
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
12 Art thou greater than our father Jacob, who gave us the well, and drank thereof himself, and his sons, and his cattle?
Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
13 Jesus answered and said to her, Every one that drinketh of this water, will thirst again;
Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
14 but whoever drinketh of the water that I will give him, will never thirst; but the water that I will give him will become within him a well of water springing up to everlasting life. (aiōn g165, aiōnios g166)
amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 The woman saith to him, Sir, give me this water, that I may not thirst, nor come hither to draw.
Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
16 He saith to her, Go, call thy husband, and come hither.
Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
17 The woman answered, I have no husband. Jesus saith to her, Thou saidst well, that thou hast no husband.
Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
18 For thou hast had five husbands; and he whom thou now hast is not thy husband; in this thou hast spoken truly.
Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
19 The woman saith to him, Sir, I perceive that thou art a prophet.
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
20 Our fathers worshipped on this mountain; and ye say, that in Jerusalem is the place where men ought to worship.
Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
21 Jesus saith to her, Believe me, woman, the hour is coming, when ye shall neither on this mountain, nor in Jerusalem, worship the Father.
Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
22 Ye worship that which ye know not; we worship that which we know; for salvation is from the Jews.
Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
23 But the hour is coming, and now is, when the true worshippers will worship the Father in spirit and in truth; for such worshippers the Father seeketh.
Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
24 God is a spirit; and they who worship must worship in spirit and in truth.
Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
25 The woman saith to him, I know that Messiah cometh (who is called Christ); when he hath come, he will tell us all things.
Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
26 Jesus saith to her, I who speak to thee am he.
Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
27 And upon this his disciples came, and marveled that he was talking with a woman. Yet no one said, What dost thou seek? or, Why dost thou talk with her?
Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
28 The woman then left her water-pot, and went away into the city, and saith to the men,
Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
29 Come, see a man who told me all things which I have done. Is this the Christ?
“Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
30 They went out of the city, and came to him.
Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
31 In the mean while the disciples asked him, saying, Rabbi, eat.
Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
32 But he said to them, I have food to eat that ye know not of.
Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
33 The disciples therefore said to one another, Hath any one brought him anything to eat?
Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
34 Jesus saith to them, My food is to do the will of him that sent me, and to finish his work.
Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
35 Do ye not say, There are yet four months, and the harvest cometh? Lo! I say to you, lift up your eyes, and look on the fields, that they are white for harvest.
Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
36 Already is the reaper receiving wages, and gathering fruit unto everlasting life; that both the sower and the reaper may rejoice together. (aiōnios g166)
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios g166)
37 And herein is fulfilled the true saying, One soweth, and another reapeth.
Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
38 I have sent you to reap that whereon ye have not labored. Others have labored, and ye have entered into their labor.
Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
39 And many of the Samaritans of that city believed in him because of the words of the woman, who testified, He told me all things which I have done.
Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
40 When therefore the Samaritans came to him, they besought him to remain with them; and he remained there two days.
To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
41 And many more believed on account of his word;
Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
42 and said to the woman, No longer do we believe on account of what thou hast told us; for we have ourselves heard him, and know that this is in truth the Saviour of the world.
Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
43 And after the two days he went from that place into Galilee.
Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
44 For Jesus himself testified, that a prophet hath no honor in his own country.
(To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
45 When therefore he came into Galilee, the Galilaeans received him, having seen all that he did in Jerusalem at the feast; for they also went to the feast.
Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
46 So he came again into Cana of Galilee, where he made the water wine. And there was a certain nobleman, whose son was sick, at Capernaum.
Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
47 He, having heard that Jesus had come out of Judaea into Galilee, went to him, and asked him to go down and heal his son; for he was at the point of death.
Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
48 Then Jesus said to him, Unless ye see signs and wonders, ye will not believe.
Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
49 The nobleman saith to him, Sir, come down before my child die.
Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
50 Jesus saith to him, Go; thy son liveth. The man believed the word that Jesus spoke to him, and went away.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
51 And as he was now going down, the servants met him, and brought word that his child was living.
Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
52 Then he inquired of them the hour when he began to mend. And they said to him, Yesterday at the seventh hour the fever left him.
Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
53 So the father knew that it was in the same hour in which Jesus said to him, Thy son is living. And he himself believed, and his whole house.
Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
54 This again, a second sign, Jesus wrought, when he had come out of Judaea into Galilee.
Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.

< John 4 >