< John 2 >

1 And on the third day there was a marriage-feast in Cana of Galilee; and the mother of Jesus was there.
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 And both Jesus and his disciples were invited to the feast.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 And they had no wine, because the wine of the feast had failed. Then the mother of Jesus saith to him, There is no wine.
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus saith to her, Woman, what have I to do with thee? My hour is not yet come.
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother saith to the servants, Whatever he saith to you, do it.
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 Now there were set there six water-pots of stone, in conformity with the Jews' custom of purifying, containing two or three firkins apiece.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus saith to them, Fill the water-pots with water. And they filled them up to the brim.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 And he saith to them, Draw out now, and bear it to the master of the feast. And they bore it.
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 But when the master of the feast tasted the water that had been made wine, not knowing whence it was, but the servants who drew the water knew, he called the bridegroom
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 and said to him, Every man setteth on the good wine first, and when men have drunk freely, that which is worse. Thou hast kept the good wine until now.
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This beginning of the signs Jesus made in Cana of Galilee, and manifested his glory; and his disciples believed in him.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 After this he went down to Capernaum, he and his mother, and his brothers, and his disciples; and they abode there not many days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 And the passover of the Jews was near; and Jesus went up to Jerusalem.
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 And he found in the temple those who sold oxen, and sheep, and doves, and the money-changers sitting.
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 And having made a scourge of cords, he drove them all out of the temple, both the sheep and the oxen; and poured out the money of the exchangers, and overthrew the tables;
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 and said to those who sold the doves, Take these things hence; make not my Father's house a house of merchandise.
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 His disciples remembered that it was written, “Zeal for thy house will consume me.”
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 The Jews therefore answered and said to him, What sign dost thou show us, seeing thou doest these things?
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered and said to them, Destroy this temple, and in three days I will raise it up.
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 Then said the Jews, Forty-six years was this temple in building; and wilt thou raise it up in three days?
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 But he spoke of the temple of his body.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 When therefore he had risen from the dead, his disciples remembered that he had said this; and they believed the Scripture, and the word which Jesus had spoken.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 And when he was in Jerusalem at the passover, at the feast, many believed in his name, when they saw his signs which he wrought.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 But Jesus did not trust himself to them, because he knew all men;
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 and had no need that any one should testify concerning man; for he himself knew what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< John 2 >