< Job 8 >
1 Then answered Bildad the Shuhite, and said:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 How long wilt thou speak such things? How long shall the words of thy mouth be like a strong wind?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Will God pervert judgment? Or will the Almighty pervert justice?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 As thy children sinned against him, He hath given them up to their transgression.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 But if thou wilt seek early to God, And make thy supplication to the Almighty, —
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 If thou wilt be pure and upright, Surely he will yet arise for thee, And prosper thy righteous habitation;
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 So that thy beginning shall be small, And thy latter end very great.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 For inquire, I pray thee, of the former age, And mark what hath been searched out by their fathers;
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 (For we are of yesterday and know nothing, Since our days upon the earth are but a shadow; )
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Will not they instruct thee, and tell thee, And utter words from their understanding?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 “Can the paper-reed grow up without mire? Can the bulrush grow without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 While it is yet in its greenness, and is not cut down, It withereth before any other herb.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Such is the fate of all who forget God; So perisheth the hope of the ungodly.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 His confidence shall come to nought, And his trust shall prove a spider's web.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He shall lean upon his house, and it shall not stand; He shall lay fast hold on it, but it shall not endure.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He is in full green before the sun, And his branches shoot forth over his garden;
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots are entwined about the heap, And he seeth the place of stones;
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 When he shall be destroyed from his place, It shall deny him, saying, 'I never saw thee.'
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Lo! such is the joy of his course! And others shall spring up from his place”
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Behold, God will not cast away an upright man; Nor will he help the evil-doers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 While he filleth thy mouth with laughter, And thy lips with gladness,
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 They that hate thee shall be clothed with shame, And the dwelling-place of the wicked shall come to nought.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”