< Job 6 >
1 Then Job answered and said:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 O that my grief were weighed thoroughly! That my calamities were put together in the balance!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Surely they would be heavier than the sand of the sea; On this account were my words rash.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For the arrows of the Almighty have pierced me; Their poison drinketh up my spirit; The terrors of God set themselves in array against me.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Doth the wild ass bray in the midst of grass? Or loweth the ox over his fodder?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Can that which is unsavory be eaten without salt? Is there any taste in the white of an egg?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 That which my soul abhorreth to touch Hath become my loathsome food.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 O that I might have my request, And that God would grant me that which I long for!
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 That it would please God to destroy me; That he would let loose his hand, and make an end of me!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Yet it should still be my consolation, Yea, in unsparing anguish I would exult, That I have not denied the commands of the Holy One.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 What is my strength, that I should hope? And what mine end, that I should be patient?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Is my strength the strength of stones? Or is my flesh brass?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Alas, there is no help within me! Deliverance is driven from me!
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 To the afflicted, kindness should be shown by a friend; Else he casteth off the fear of the Almighty.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 But my brethren are faithless like a brook; Like streams of the valley that pass away;
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Which are turbid by reason of the ice, And the snow, which hideth itself in them.
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 As soon as they flow forth, they vanish; When the heat cometh, they are dried up from their place.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 The caravans turn aside to them on their way; They go up into the desert, and perish.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 The caravans of Tema look for them; The companies of Sheba expect to see them;
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 They are ashamed that they have relied on them; They come to their place, and are confounded.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 So ye also are nothing; Ye see a terror, and shrink back.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Have I said, Bring me gifts? Or, Give a present for me out of your substance?
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Or, Deliver me from the enemy's hand? Or, Rescue me from the hand of the violent?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Convince me, and I will hold my peace; Cause me to understand wherein I have erred.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 How powerful are the words of truth! But what do your reproaches prove?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Do ye mean to censure words? The words of a man in despair are but wind.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Truly ye spread a net for the fatherless; Ye dig a pit for your friend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Look now upon me, I pray you; For to your very face can I speak falsehood?
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Return, I pray, and let there be no unfairness; Yea, return; —still is my cause righteous.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Is there iniquity on my tongue? Cannot my taste discern what is sinful?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?