< Job 4 >

1 Then spake Eliphaz the Temanite, and said:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 If one attempt a word with thee, wilt thou be offended? But who can refrain from speaking?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Behold, thou hast admonished many; Thou hast strengthened feeble hands;
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Thy words have upheld him that was falling, And thou hast given strength to feeble knees.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 But now it is come upon thee, and thou faintest; It toucheth thee, and thou art confounded!
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Is not thy fear of God thy hope, And the uprightness of thy ways thy confidence?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Remember, I pray thee, who ever perished being innocent? Or where have the righteous been cut off?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 According to what I have seen, they who plough iniquity, And sow mischief, reap the same.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 By the blast of God they perish, And by the breath of his nostrils they are consumed.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 The roaring of the lion, and the voice of the fierce lion, And the teeth of the young lions are broken.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 The fierce lion perisheth for lack of prey, And the whelps of the lioness are scattered abroad.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 A word was once secretly brought to me, And mine ear caught a whisper thereof.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 Amid thoughts from visions of the night, When deep sleep falleth upon men,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 A fear and a horror came upon me, Which made all my bones to shake.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Then a spirit passed before my face, The hair of my flesh rose on end;
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 It stood still, but its form I could not discern; An image was before mine eyes; There was silence, and I heard a voice:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 “Shall mortal man be more just than God? Shall man be more pure than his Maker?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Behold, he putteth no trust in his ministering spirits, And his angels he chargeth with frailty.
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 What then are they who dwell in houses of clay, Whose foundation is in the dust, Who crumble to pieces, as if moth-eaten!
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Between morning and evening are they destroyed; They perish for ever, and none regardeth it.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 The excellency that is in them is torn away; They die before they have become wise.”
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >