< Job 36 >
1 Elihu also proceeded, and said:
Elihu ya ci gaba,
2 Bear with me a little while, that I may show thee! For I have yet words in behalf of God.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will bring my knowledge from afar, And assert the justice of my Maker.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Truly my words shall not be false: A man of sound knowledge is before thee.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Behold, God is great, but despiseth not any; Great is he in strength of understanding.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He suffereth not the wicked to prosper, But rendereth justice to the oppressed.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He withdraweth not his eyes from the righteous; But establisheth them for ever with kings on the throne, That they may be exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And if they be bound in fetters, And holden in the cords of affliction,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Then showeth he them their deeds, And how they have set him at defiance by their transgressions;
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 He also openeth their ears to admonition, And commandeth them to return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they obey and serve him, They spend their days in prosperity, And their years in pleasures.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they obey not, they perish by the sword; They die in their own folly.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 The corrupt in heart treasure up wrath; They cry not to God, when he bindeth them.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 They die in their youth; They close their lives with the unclean.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 But he delivereth the poor in their distress; He openeth their ears in affliction.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 He will bring thee also from the jaws of distress To a broad place, where is no straitness; And the provision of thy table shall be full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 But if thou art full of the judgment of the wicked, Judgment and justice shall take hold of thee.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 For if wrath be with him, beware lest he take thee away by his stroke, So that a great ransom shall not save thee!
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Will he esteem thy riches? No! neither thy gold, nor all the abundance of thy wealth.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Long not thou for that night To which nations are taken away from their place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed, turn not thine eyes to iniquity! For this hast thou chosen rather than affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Behold, God is exalted in his power: Who is a teacher like him?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who hath prescribed to him his way? Or who can say to him, “Thou hast done wrong”?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Forget not to magnify his work, Which men celebrate with songs.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All mankind gaze upon it; Mortals behold it from afar.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Behold, God is great; we cannot know him, Nor search out the number of his years.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Lo! he draweth up the drops of water, Which distil rain from his vapor;
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 The clouds pour it down, And drop it upon man in abundance.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Who can understand the spreading of his clouds, And the rattling of his pavilion?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Behold, he spreadeth around himself his light, And he clotheth himself with the depths of the sea.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 By these he punisheth nations, And by these he giveth food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 His hands he covereth with lightning; He giveth it commandment against an enemy.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 His thunder maketh him known; Yea, to the herds, as he ascendeth on high.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.