< Job 35 >
1 Moreover Elihu proceeded, and said:
Sai Elihu ya ce,
2 Dost thou then think this to be right? Thou hast said, “I am more righteous than God.”
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 For thou askest, “What advantage have I? What have I gained, more than if I had sinned?”
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 I will answer thee, And thy companions with thee.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Look up to the heavens, and see! And behold the clouds, which are high above thee!
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 If thou sinnest, what doest thou against Him? If thy transgressions be multiplied, what doest thou to him?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 If thou art righteous, what dost thou give him? Or what receiveth he at thy hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Thy wickedness injureth only a man like thyself, And thy righteousness profiteth only a son of man.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 The oppressed cry out on account of the multitude of wrongs; They cry aloud on account of the arm of the mighty.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 But none saith, “Where is God, my Maker, Who giveth songs in the night;
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Who teacheth us more than the beasts of the earth, And maketh us wiser than the birds of heaven?”
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There they cry aloud on account of the pride of the wicked; But he giveth no answer.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 For God will not hear the vain supplication, Nor will the Almighty regard it;
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Much less when thou sayest thou canst not see him: Justice is with him, —only wait thou for him!
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 But now, because he hath not visited in his anger, Nor taken strict note of transgression,
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Therefore hath Job opened his mouth rashly, And multiplied words without knowledge.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”