< Job 3 >

1 At length Job opened his mouth, and cursed the day of his birth.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 And Job spake and said:
Ayuba ya ce,
3 Perish the day in which I was born, and the night which said, “A man-child is conceived!”
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Let that day be darkness; Let not God seek it from above; Yea, let not the light shine upon it!
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Let darkness and the shadow of death redeem it; Let a cloud dwell upon it; Let whatever darkeneth the day terrify it!
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 As for that night, let darkness seize upon it; Let it not rejoice among the days of the year; Let it not come into the number of the months!
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 O let that night be unfruitful! Let there be in it no voice of joy;
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Let them that curse the day curse it, Who are skilful to stir up the leviathan!
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Let the stars of its twilight be darkened; Let it long for light, and have none; Neither let it see the eyelashes of the morning!
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 Because it shut not up the doors of my mother's womb, And hid not trouble from mine eyes.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 Why died I not at my birth? Why did I not expire when I came forth from the womb?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 Why did the knees receive me, And why the breasts, that I might suck?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 For now should I lie down and be quiet; I should sleep; then should I be at rest,
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 With kings and counsellors of the earth, Who built up for themselves—ruins!
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 Or with princes that had gold, And filled their houses with silver;
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 Or, as a hidden untimely birth, I had perished; As infants which never saw the light.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 There the wicked cease from troubling; There the weary are at rest.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 There the prisoners rest together; They hear not the voice of the oppressor.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 The small and the great are there, And the servant is free from his master.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 Why giveth He light to him that is in misery, And life to the bitter in soul,
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 Who long for death, and it cometh not, And dig for it more than for hid treasures;
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 Who rejoice exceedingly, Yea, exult, when they can find a grave?
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 Why is light given to a man from whom the way is hid, And whom God hath hedged in?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 For my sighing cometh before I eat, And my groans are poured out like water.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 For that which I dread overtaketh me; That at which I shudder cometh upon me.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 I have no peace, nor quiet, nor respite: Misery cometh upon me continually.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >