< Job 29 >

1 Moreover Job continued his discourse, and said:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 O that I were as in months past, In the days when God was my guardian;
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 When his lamp shined over my head, And when by his light I walked through darkness!
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 As I was in the autumn of my days, When the friendship of God was over my tent;
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 When the Almighty was yet with me, And my children were around me;
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 When I bathed my steps in milk, And the rock poured me out rivers of oil!
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 When I went forth to the gate by the city, And took my seat in the market-place,
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 The young men saw me and hid themselves, And the aged arose and stood.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 The princes refrained from speaking, And laid their hand upon their mouth.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 The nobles held their peace, And their tongue cleaved to the roof of their mouth.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 When the ear heard me, then it blessed me; And when the eye saw me, it gave witness to me.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 For I delivered the poor, when they cried; And the fatherless, who had none to help him.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 The blessing of him that was ready to perish came upon me, And I caused the heart of the widow to sing for joy.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 I clothed myself with righteousness, and it clothed itself with me; And justice was my robe and diadem.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 I was eyes to the blind, And feet was I to the lame;
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 I was a father to the poor, And the cause of him I knew not I searched out;
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 And I broke the teeth of the wicked, And plucked the spoil from his jaws.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Then said I, “I shall die in my nest; I shall multiply my days as the sand.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 My root is spread abroad to the waters, And the dew abideth on my branches.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 My glory is fresh with me, And my bow gathereth strength in my hand.”
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 To me men gave ear, and waited, And kept silence for my counsel.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 To my words they made no reply, When my speech dropped down upon them.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 Yea, they waited for me as for the rain; They opened their mouths wide as for the latter rain.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 If I smiled upon them, they believed it not; Nor did they cause the light of my countenance to fall.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 When I came among them, I sat as chief; I dwelt as a king in the midst of an army, As a comforter among mourners.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >