< Job 27 >

1 Moreover Job continued his discourse, and said:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 As God liveth, who hath rejected my cause, And the Almighty, who hath afflicted my soul;
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 As long as my breath is in me, And the spirit of God is in my nostrils,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Never shall my lips speak falsehood, Nor my tongue utter deceit.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 God forbid that I should acknowledge you to be just: To my last breath will I assert my integrity.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 I will hold fast my innocence, and not let it go; My heart reproacheth me for no part of my life.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 May mine enemy be as the wicked, And he that riseth up against me as the unrighteous!
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 For what is the hope of the wicked, when God cutteth off his web, And taketh away his life?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Will he listen to his cry, When trouble cometh upon him?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Can he delight himself in the Almighty, And call at all times upon God?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 I will teach you concerning the hand of God; That which is with the Almighty I will not conceal.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Behold, ye yourselves have all seen it; Why then do ye cherish such vain thoughts?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 This is the portion of the wicked man from God, —The inheritance which oppressors receive from the Almighty.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 If his children be multiplied, it is for the sword; And his offspring shall not be satisfied with bread.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Those of them that escape shall be buried by Death, And their widows shall not bewail them.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Though he heap up silver as dust, And procure raiment as clay, —
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 He may procure, but the righteous shall wear it, And the innocent shall share the silver.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 He buildeth his house like the moth, Or like the shed which the watchman maketh.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 The rich man lieth down, and is not buried; In the twinkling of an eye he is no more.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Terrors pursue him like a flood; A tempest stealeth him away in the night.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 The east wind carrieth him away, and he perisheth; Yea, it sweepeth him away from his place.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 God sendeth his arrows at him, and doth not spare; He would fain escape from His hand.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Men clap their hands at him, And hiss him away from his place.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >