< Job 21 >

1 But Job answered and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hear attentively my words, And let this be your consolation.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Bear with me, that I may speak; And after I have spoken, mock on!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Is my complaint concerning man? Why then should I not be angry?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Look upon me, and be astonished, And lay your hand upon your mouth!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 When I think of it, I am confounded; Trembling taketh hold of my flesh.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Why is it that the wicked live, Grow old, yea, become mighty in substance?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Their children are established in their sight with them, And their offspring before their eyes.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses are in peace, without fear, And the rod of God cometh not upon them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Their bull gendereth, and faileth not; Their cow calveth, and casteth not her calf.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 They send forth their little ones like a flock, And their children dance.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They sing to the timbrel and harp, And rejoice at the sound of the pipe.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 They spend their days in prosperity, And in a moment go down to the under-world. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 And yet they say unto God, “Depart from us! We desire not the knowledge of thy ways!
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Who is the Almighty, that we should serve him? And what will it profit us, if we pray to him?”
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 [[Ye say, ]] “Lo! their prosperity is not secure in their hands! Far from me be the conduct of the wicked!”
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How often is it, that the lamp of the wicked is put out? And that destruction cometh upon them, And that He dispenseth to them tribulations in his anger?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 How often are they as stubble before the wind, Or as chaff, which the whirlwind carrieth away?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 “But” [[say ye]] “God layeth up his iniquity for his children.” Let him requite the offender, and let him feel it!
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Let his own eyes see his destruction, And let him drink of the wrath of the Almighty!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what concern hath he for his household after him, When the number of his own months is completed?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Who then shall impart knowledge to God, —To him that judgeth the highest?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 One dieth in the fulness of his prosperity, Being wholly at ease and quiet;
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His sides are full of fat, And his bones moist with marrow.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Another dieth in bitterness of soul, And hath not tasted pleasure.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Alike they lie down in the dust, And the worms cover them.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Behold, I know your thoughts, And the devices by which ye wrong me.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For ye say, “Where is the house of the oppressor, And where the dwelling-places of the wicked?”
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Have ye never inquired of travellers, And do ye not know their tokens,
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 That the wicked is spared in the day of destruction, And that he is borne to his grave in the day of wrath?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Who will charge him with his conduct to his face, And who will requite him for the evil he hath done?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Even this man is borne with honor to the grave; Yea, he watcheth over his tomb.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Sweet to him are the sods of the valley: And all men move after him, As multitudes without number before him.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Why then do ye offer your vain consolations? Your answers continue false.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >