< Job 20 >

1 Then answered Zophar the Naamathite, and said:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 For this do my thoughts lead me to reply, And for this is my ardor within me.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 I have heard my shameful rebuke; And the spirit, from my understanding, answereth for me.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Knowest thou not, that from the days of old, From the time when man was placed upon the earth,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 The triumphing of the wicked hath been short, And the joy of the impious but for a moment?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Though his greatness mount up to the heavens, And his head reach to the clouds,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Yet shall he perish for ever, and be mingled with dust; They who saw him shall say, Where is he?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 He shall flee away like a dream, and shall not be found; Yea, he shall disappear like a vision of the nigh.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 The eye also which saw him shall see him no more, And his dwelling-place shall never more behold him.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 His sons shall seek the favor of the poor, And their hands shall give back his wealth.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 His bones are full of his youth, But they shall lie down with him in the dust.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Though wickedness be sweet in his mouth, Though he hide it under his tongue,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 Though he cherish it, and will not part with it, And keep it fast in his mouth,
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Yet his meat shall be changed within him, And become to him the poison of asps.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 He hath glutted himself with riches, And he shall throw them up again; Yea, God shall cast them out of his body.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 He shall suck the poison of asps; The tongue of the viper shall destroy him.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 He shall never see the flowing streams, And the rivers of honey and milk.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 The fruits of his toil he shall give back, and shall not enjoy them: It is substance to be restored, and he shall not rejoice therein.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Because he hath oppressed and abandoned the poor, And seized upon the house which he did not build;
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Because he knew no rest in his bosom, He shall not save that in which he delighteth.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Because nothing escaped his greediness, His prosperity shall not endure.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 In the fulness of his abundance he shall be brought low; Every hand of the wretched shall come upon him.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 He shall, indeed, have wherewith to fill himself: God shall send upon him the fury of his anger, And rain it down upon him for his food.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 If he fleeth from the iron weapon, The bow of brass shall pierce him through.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 He draweth the arrow, and it cometh forth from his body; Yea, the glittering steel cometh out of his gall. Terrors are upon him;
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Calamity of every kind is treasured up for him. A fire not blown shall consume him; It shall consume whatever is left in his tent.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 The heavens shall reveal his iniquity, And the earth shall rise up against him.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 The substance of his house shall disappear; It shall flow away in the day of His wrath.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Such is the portion of the wicked man from God, And the inheritance appointed for him by the Almighty.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >