< Job 2 >
1 Again there was a day when the sons of God came to present themselves before Jehovah; and Satan came also among them to present himself before Jehovah.
Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
2 And Jehovah said to Satan, Whence comest thou? And Satan answered Jehovah, and said, From wandering over the earth, and walking up and down in it.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
3 Then said Jehovah to Satan, Hast thou observed my servant Job, that there is none like him upon the earth, an upright and good man, fearing God and departing from evil? And still he holdeth fast his integrity, although thou didst excite me against him to destroy him without a cause.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
4 And Satan answered Jehovah, and said, Skin for skin, yea, all that a man hath will he give for his life.
Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
5 But put forth now thy hand, and touch his bone and his flesh, and to thy face will he renounce thee.
Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
6 And Jehovah said to Satan, Behold, he is in thy hand; but spare his life.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
7 Then Satan went forth from the presence of Jehovah, and smote Job with sore boils from the sole of his foot to his crown.
Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
8 And he took a potsherd to scrape himself withal, and sat down among the ashes.
Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
9 Then said his wife to him, Dost thou still retain thine integrity? Renounce God, and die.
Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
10 But he said to her, Thou talkest like one of the foolish women. What! shall we receive good at the hand of God, and shall we not receive evil? In all this, Job sinned not with his lips.
Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
11 Now three friends of Job heard of all this evil that had come upon him, and came each one from his home; Eliphaz the Temanite, and Bildad the Shuhite, and Zophar the Naamathite; for they had agreed to come to mourn with him, and to comfort him.
Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
12 And they lifted up their eyes at a distance, and knew him not; then they raised their voices and wept, and rent each one his mantle, and sprinkled dust upon their heads toward heaven.
Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
13 And they sat down with him upon the ground seven days and seven nights, and none spake a word to him; for they saw that his grief was very great.
sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.