< Job 16 >

1 But Job answered and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Of such things as these I have heard enough! Miserable comforters are ye all!
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Will there ever be an end to words of wind? What stirreth thee up, that thou answerest?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 I also might speak like you, If ye were now in my place; I might string together words against you, And shake my head at you.
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 I would strengthen you with my mouth, And the consolation of my lips should sustain you.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 If I speak, my grief is not assuaged; And if I forbear, it doth not leave me.
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 For now He hath quite exhausted me; Thou hast desolated all my house!
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Thou hast seized hold of me, and this is a witness against me; My leanness riseth up and testifieth against me to my face.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 His anger teareth my flesh, and pursueth me; He gnasheth upon me with his teeth; My adversary sharpeneth his eyes upon me.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 They gape for me with their mouths; In scorn they smite me on the cheek; With one consent they assemble against me.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 God hath given me a prey to the unrighteous, And delivered me into the hands of the wicked.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 I was at ease, but he hath crushed me; He hath seized me by the neck, and dashed me in pieces; He hath set me up for his mark.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 His archers encompass me around; He pierceth my reins, and doth not spare; He poureth out my gall upon the ground.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 He breaketh me with breach upon breach; He rusheth upon me like a warrior.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 I have sewed sackcloth upon my skin, And thrust my horn into the dust.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 My face is red with weeping, And upon my eyelids is deathlike darkness.
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Yet is there no injustice in my bands. And my prayer hath been pure.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 O earth! cover not thou my blood, And let there be no hiding-place for my cry!
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Yet even now, behold, my witness is in heaven, And he who knoweth me is on high.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 My friends have me in derision, But my eye poureth out tears unto God.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 O that one might contend for a man with God, As a man contendeth with his neighbor!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 For when a few years shall have passed, I shall go the way whence I shall not return.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.

< Job 16 >