< Jeremiah 41 >
1 And it came to pass in the seventh month, that Ishmael, the son of Nethaniah, the son of Elishama, of the blood royal, and one of the great officers of the king, and ten men with him, came to Gedaliah, the son of Ahikam, to Mizpah; and they ate bread there together in Mizpah.
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 Then Ishmael, the son of Nethaniah, arose, and the ten men that were with him, and smote Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, with the sword, and slew him whom the king of Babylon had made governor over the land.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 And all the Jews that were with him, with Gedaliah at Mizpah, and the Chaldaeans that were found there, the men of war, did Ishmael smite.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 And it came to pass, the second day after he had slain Gedaliah, and no man knew it,
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 that there came certain men from Shechem, from Shiloh, and from Samaria, fourscore persons, having their beards shaven, and their clothes rent, and having cut themselves, with an oblation and incense in their hands, to bring to the house of Jehovah.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 And Ishmael, the son of Nethaniah, went forth from Mizpah to meet them, weeping all along as he went; and when he met them, he said to them, “Come ye to Gedaliah, the son of Ahikam.”
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 And when they had come into the midst of the city, Ishmael, the son of Nethaniah, slew them, and cast them into the pit, he and the men that were with him.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 But ten men were found among them who said to Ishmael, “Slay us not, for we have hidden stores in the field, of wheat, and barley, and oil, and honey.” He forbore, therefore, and slew them not with their brethren.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 Now the pit into which Ishmael cast all the dead bodies of the men whom he slew, together with Gedaliah, is the same which King Asa made on account of Baasha, king of Israel; and Ishmael, the son of Nethaniah, filled it with them that were slain.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 And Ishmael took captive all the residue of the people that were in Mizpah, the king's daughters, and all the people that remained in Mizpah, whom Nebuzaradan, captain of the guard, had committed to the charge of Gedaliah, the son of Ahikam; even Ishmael, the son of Nethaniah, took them captive, and set forth to go over [[the Jordan]] to the children of Ammon.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 But when Johanan, the son of Kareah, and all the captains of the forces that were with him, heard of all the evil which Ishmael, the son of Nethaniah, had done,
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 they took all the men, and went up to fight with Ishmael, the son of Nethaniah, and came up with him at the great waters that are in Gibeon.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 And when all the people which were with Ishmael saw Johanan, the son of Kareah, and all the captains of the forces that were with him, they were glad;
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 and all the people that Ishmael had carried away captive from Mizpah faced about and returned, and went to Johanan, the son of Kareah.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 But Ishmael, the son of Nethaniah, escaped from Johanan with eight men, and went to the children of Ammon.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 Then took Johanan, the son of Kareah, and all the captains of the forces that were with him, all the remnant of the people whom he had recovered from Ishmael, the son of Nethaniah, from Mizpah, after he had slain Gedaliah, the son of Ahikam, strong men, men of war, and women, and children, and eunuchs, whom he had brought back from Gibeon;
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 and they went, and tarried in the inn of Chimham, which is near Bethlehem, in order to flee into Egypt
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 from the Chaldaeans; for they were afraid of them, because Ishmael, the son of Nethaniah, had slain Gedaliah, the son of Ahikam, whom the king of Babylon had made governor over the land.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.