< Jeremiah 34 >
1 The word which came to Jeremiah from Jehovah, when Nebuchadnezzar, king of Babylon, and all his army, and all the kingdoms of the earth that were under his dominion, and all the nations, made war against Jerusalem, and against all the cities thereof, saying: —
Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Thus saith Jehovah, the God of Israel: Go and speak to Zedekiah, the king of Judah, and say to him, Thus saith Jehovah: Behold, I will give this city into the hand of the king of Babylon, and he shall burn it with fire.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
3 And thou shalt not escape out of his hand, but shalt surely be taken and delivered into his hand; and thine eyes shall behold the eyes of the king of Babylon, and he shall speak with thee mouth to mouth, and thou shalt go to Babylon.
Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
4 Yet hear the word of Jehovah, O Zedekiah, king of Judah! Thus saith Jehovah concerning thee: Thou shalt not die by the sword;
“‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
5 in peace shalt thou die; and according to the burnings of thy fathers, the former kings, who were before thee, so shall they burn for thee; and they shall lament for thee, saying, “Ah, lord!” for I have spoken the word, saith Jehovah.
za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
6 And Jeremiah the prophet spake all these words to Zedekiah, king of Judah, at Jerusalem.
Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
7 And the army of the king of Babylon fought against Jerusalem, and against all the cities of Judah that were left, against Lachish, and against Azekah; for these fortified cities remained of the cities of Judah.
yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
8 The word which came to Jeremiah from Jehovah, after King Zedekiah had made a covenant with all the people that were at Jerusalem, to proclaim liberty to them,
Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
9 that every one should let his man-servant or his maid-servant, being a Hebrew or Hebrewess, go free, that no one should retain his brother, a Jew, in servitude.
Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
10 And all the princes, and all the people, who had entered into covenant to let every one his man-servant and every one his maid-servant go free, and retain them in servitude no longer, obeyed; they obeyed, and let them go.
Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
11 But they returned afterwards, and took back the men-servants and the maid-servants whom they had let go free, and brought them into subjection as men-servants and as maid-servants.
Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
12 Then came the word of Jehovah to Jeremiah from Jehovah, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Thus saith Jehovah, the God of Israel: I made a covenant with your fathers in the day when I brought them forth out of the land of Egypt, out of the house of bondmen, and said,
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
14 “At the end of seven years ye shall let go every man his brother, a Hebrew, who shall have been sold to thee; when he shall have served thee six years, thou shalt let him go free from thee.” But your fathers hearkened not to me, nor inclined their ear.
‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
15 And when ye had turned at this time, and had done what was right in mine eyes, in proclaiming liberty every one to his neighbor, and had entered into a covenant before me in the house which is called by my name,
Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
16 then ye returned and profaned my name, and took back every one his man-servant, and every one his maid-servant, whom he had set at liberty at their pleasure, and brought them into subjection to be men-servants and maid-servants to you.
Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
17 Therefore thus saith Jehovah: Ye have not hearkened to me in proclaiming liberty every one to his brother, and every one to his neighbor. Behold, I proclaim a liberty for you, saith Jehovah, to the sword, to pestilence, and to famine, and I will give you up to oppression in all the kingdoms of the earth;
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
18 and I will make the men who have transgressed my covenant, who have not performed the words of the covenant which they made before me, like the calf which they cut in twain, and passed between the parts thereof,
Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
19 the princes of Judah, and the princes of Jerusalem, the eunuchs, and the priests, and all the people of the land, that passed between the parts of the calf.
Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
20 I will give them into the hand of their enemies, and into the hand of them that seek their life; and their dead bodies shall be food for the birds of heaven, and for the beasts of the earth.
zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
21 And Zedekiah, king of Judah, and his princes, will I give into the hand of their enemies, and into the hand of them that seek their life, even into the hand of the king of Babylon's army, which are gone up from you.
“Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
22 Behold, I will command, saith Jehovah, and cause them to return to this city, and they shall fight against it, and take it, and burn it with fire; and I will make the cities of Judah a desolation without an inhabitant.
Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”