< Jeremiah 30 >
1 The word which came to Jeremiah from Jehovah, saying: —
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Thus saith Jehovah, the God of Israel: Write thee all the words which I have spoken to thee in a book.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 For behold the days come, saith Jehovah, when I will bring back the captives of my people Israel and Judah, saith Jehovah, and cause them to return to the land which I gave to their fathers, and they shall possess it.
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 And these are the words which Jehovah spake concerning Israel and concerning Judah.
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 Behold, thus saith Jehovah: The voice of trembling do we hear; There is alarm, and no peace.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Ask ye now and see, Whether a male doth bring forth? Why then do I see every man's hands upon his loins, like a woman in travail? And why are all faces turned into paleness?
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Alas! that day is great, So that there is none like it; It is a time of trouble for Jacob, Yet shall he be saved from it.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 For in that day, saith Jehovah of hosts, I will break his yoke from his neck, And his bands will I burst asunder, And he shall be subject to strangers no more.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 But they shall serve Jehovah, their God, And David, their king, whom I will raise up for them.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 Therefore fear thou not, O my servant Jacob, saith Jehovah, And be not thou dismayed, O Israel! For, behold, I will bring thee safe from afar, And thy posterity from the land of their captivity; And Jacob shall return, and be at rest; Yea, he shall be quiet, and none shall make him afraid.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 For I will be with thee, saith Jehovah, to save thee; When I shall make a full end of all the nations Whither I have dispersed thee, Yet will I not make a full end of thee; I will correct thee in measure, Yet must I not leave thee wholly unpunished.
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 For thus saith Jehovah: Thy bruise is incurable; Thy wound is mortal.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 No one offereth his help for thy cure; No healing medicines are applied to thee.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 All thy lovers have forgotten thee; They inquire not after thee. For with the wound of an enemy have I smitten thee, With the chastisement of a cruel one, For the multitude of thine iniquities, Because thy sins were increased.
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Why criest thou because of thy bruise? Thy pain is without remedy. For the multitude of thine iniquities, Because thy sins were increased, Have I done these things to thee.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Yet all they that devour thee shall be devoured, And all thine enemies, yea, all of them, shall go into captivity, And they that spoil thee shall become a spoil, And all that plunder thee will I give up to plunder.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 For I will restore soundness to thee, And I will heal thee of thy wounds, saith Jehovah; For they have called thee the outcast, Zion, whom no man careth for.
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Thus saith Jehovah: Behold, I will bring back the captives of the tents of Jacob, And I will have pity upon his dwelling-places, And the city shall be builded upon her heap, And the palace shall be inhabited as of old.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 And out of them shall go forth thanksgiving, And the voice of them that make merry. And I will multiply them, and they shall not be few, And I will exalt them, and they shall not be low.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 And their children shall be as aforetime, And their congregation shall be established before me, And I will punish all that oppress them.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 And their princes shall be of themselves, And their governor shall proceed from the midst of them. And I will cause them to approach, and they shall come near to me; For who is he that would dare to come near to me? saith Jehovah.
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 And ye shall be my people, And I will be your God.
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 Behold, a whirlwind from Jehovah, Furious doth it go forth, Even a sweeping whirlwind; Upon the head of the wicked shall it rush.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 The fierce anger of Jehovah shall not turn back Until he shall have executed, until he shall have accomplished, the purpose of his heart; In a future day ye shall understand it fully.
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.