< James 1 >
1 James, a servant of God and of the Lord Jesus Christ, to the twelve tribes which are scattered abroad, greeting.
Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
2 Count it all joy, my brethren, when ye fall into various temptations;
Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
3 knowing that the trying of your faith worketh endurance.
domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
4 But let endurance have a perfect work, that ye may be perfect and entire, wanting in nothing.
Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
5 But if any one of you is wanting in wisdom, let him ask of God, who giveth to all liberally, and upbraideth not; and it will be given him.
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
6 But let him ask in faith, nothing doubting; for he that doubteth is like a wave of the sea driven by the wind and tossed.
Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
7 For let not that man think that he shall receive anything from the Lord,
Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
8 a double-minded man as he is, unstable in all his ways.
shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
9 Let the brother of low degree glory in that he is exalted;
Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
10 but the rich, in that he is made low; because as the flower of the grass he will pass away.
Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
11 For the sun rose with its burning heat, and withered the grass, and its flower fell off, and the beauty of its appearance perished; so also will the rich man fade away in his ways.
Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
12 Blessed is the man that endureth temptation; for when he is approved, he will receive the crown of life, which He promised to them that love him.
Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
13 Let no one when he is tempted, say, I am tempted by God; for God cannot be tempted with evil, and he tempteth no one.
Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
14 But each one is tempted when by his own lust he is led away and enticed;
amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
15 then lust, having conceived, bringeth forth sin, and sin, when completed, bringeth forth death.
Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
16 Do not err, my beloved brethren.
Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
17 Every good gift and every perfect gift is from above, coming down from the Father of the lights, with whom is no change, nor shadow from turning.
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
18 Of his own will he begot us with the word of truth, that we should be a kind of first-fruits of his creatures.
Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
19 Wherefore, my beloved brethren, let every man be swift to hear, slow to speak, slow to wrath.
’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
20 For the wrath of man worketh not the righteousness of God.
gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
21 Wherefore put off all filthiness, and excess of wickedness, and receive with meekness the implanted word, which is able to save your souls.
Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
22 But be doers of the word, and not hearers only, deceiving yourselves.
Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
23 For if any one is a hearer of the word, and not a doer, he is like a man beholding his natural face in a glass;
Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
24 for he beholds himself, and goes away, and immediately forgets what manner of man he was.
bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
25 But he who looks into the perfect law of liberty, and remains there, being not a forgetful hearer, but a doer of the work, this man will be blessed in his deed.
Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
26 If any one thinks that he is religious, and bridles not his tongue, but deceives his own heart, this man's religion is vain.
In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
27 Pure religion and undefiled before God, the Father, is this, to visit the fatherless and widows in their affliction, and to keep one's self unspotted from the world.
Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.