< Isaiah 57 >

1 The righteous man perisheth, and no one layeth it to heart; And pious men are taken away, and none considereth That because of the evil the righteous man is taken away.
Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
2 He entereth into peace; He resteth in his bed, Every one that walketh in uprightness.
Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
3 But draw near hither, ye sons of the sorceress, Ye brood of the adulterer and the harlot!
“Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
4 Of whom do ye make your sport, And at whom do ye make wide the mouth, And draw out the tongue? Are ye not rebellious children, a treacherous brood?
Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
5 Burning with lust for idols Under every green tree, Slaying children in the valleys, Under the clefts of the rocks?
Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
6 With the smooth stones of the valley is thy portion; These, these are thy lot; Here thou pourest out thy drink-offering, And presentest thy meat-offering; Can I see such things, and be at rest?
Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
7 Upon a high and lofty mountain settest thou thy bed; Thither dost thou go up to offer sacrifice;
Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
8 Behind the doors and the posts dost thou place thy memorial; Thou departest from me, and uncoverest, and ascendest, and enlargest thy bed. Thou makest an agreement with them; Thou desirest their bed; Thou choosest a place.
A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
9 Thou goest to the king with oil, And takest much precious perfume; Thou sendest thine ambassadors afar, Yea, down to the under-world. (Sheol h7585)
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol h7585)
10 In the length of thy journeys thou hast wearied thyself, But thou sayest not, “I will desist”; Thou yet findest life in thy hand, Therefore thou art not discouraged.
Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
11 On account of whom art thou anxious, and of whom art thou afraid, that thou hast proved false, And hast not remembered me, nor laid it to heart? Behold, I have been silent a long time; Therefore thou fearest me not.
“Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
12 But now I announce thy deliverance, And thy works do not profit thee.
Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
13 When thou criest, let thy host of idols deliver thee! But the wind shall bear them all away; A breath shall take them off; But he that putteth his trust in me Shall possess the land, And shall inherit my holy mountain.
Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
14 Men shall say, Cast up, cast up, prepare the road; Remove every obstruction from the way of my people!
Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
15 For thus saith the high and lofty One That inhabiteth eternity, whose name is Holy: I dwell in the high and holy place; With him also that is of a contrite and humble spirit; To revive the spirit of the humble, And to revive the heart of the contrite ones.
Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
16 For I will not contend forever, Nor will I be always angry; For life would fail before me, And the souls which I created.
Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
17 For the guilt of his covetousness I was angry; I smote him, I hid myself, and was angry; But yet he went on perversely in the way of his heart.
Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
18 I have seen his ways, yet will I heal him; I will guide him, and I will restore comfort To him and to his mourners;
Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
19 I create the fruit of the lips. Peace, peace to him that is far off, and to him that is nigh, Saith Jehovah; I will heal him.
ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
20 But the wicked is like the troubled sea, Which cannot rest, Whose waters cast up mire and dirt.
Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
21 There is no peace, saith my God, for the wicked.
“Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.

< Isaiah 57 >