< Isaiah 32 >

1 Behold! a king shall reign in righteousness, And princes shall rule with equity.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 Every one of them shall be a hiding-place from the wind, And a shelter from the tempest; As streams of water in a dry place, As the shadow of a great rock in a weary land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 The eyes of them that see shall no more be blind, And the ears of them that hear shall hearken.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 The heart of the rash shall gain wisdom, And the tongue of the stammerer learn to speak plainly.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 The vile shall no more be called liberal, Nor the niggard said to be bountiful;
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 For the vile will still utter villany, And his heart will devise iniquity; He will practise deception, and speak impiety against God; He will take away the food of the hungry, And deprive the thirsty of drink.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 The instruments also of the niggard are evil; He plotteth mischievous devices, To destroy the poor with lying words, Even when the cause of the needy is just.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 But the liberal deviseth liberal things, And in liberal things will he persevere.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 Arise, hear my voice, ye women that are at ease! Give ear to my speech, ye careless daughters!
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 One year more, and ye shall tremble, ye careless women! For the vintage shall fail; the harvest shall not come.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Tremble, O ye that are at ease! Be in dismay, ye careless ones! Strip you, make you bare, gird ye sackcloth upon your loins!
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 They shall smite themselves on their breasts, On account of the pleasant fields, On account of the fruitful vine.
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 Upon the land of my people shall come up thorns and briers; Yea, upon all the houses of joy in the joyous city.
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 For the palace shall be forsaken; The tumult of the city shall be solitary; The fortified hill and the tower shall be dens forever; The joy of wild-asses, the pasture of flocks;
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 Until the spirit from on high be poured upon us, And the wilderness become a fruitful field, And the fruitful field be esteemed a forest.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 Then shall justice dwell in the wilderness, And righteousness in the fruitful field.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 And the effect of righteousness shall be peace, And the fruit of righteousness quiet and security forever.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 Then shall my people dwell in peaceful habitations, In secure dwellings, in quiet resting-places.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 But the hail shall descend, and the forest shall fall; And the city shall be brought very low.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Happy ye who sow beside all waters; Who send forth thither the feet of the ox and the ass!
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.

< Isaiah 32 >