< Hosea 8 >
1 Put the trumpet to thy mouth! Like an eagle cometh an enemy against the house of Jehovah, Because they have transgressed my covenant, And have rebelled against my law.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 They shall say to me, My God, we know thee, we, thine Israel!
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 Israel hath cast away what is good; The enemy shall pursue him.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 They have set up kings, but not by me; They have made princes, and I knew it not. Of their silver and their gold have they made themselves idols, That they may be brought to destruction.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 An abomination is thy calf, O Samaria! Mine anger is kindled against them; How long will it be ere they can attain to purity!
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 For from Israel it came; The workman made it, and it is no God; Yea, into fragments shall the calf of Samaria be broken.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 They have sown the wind, And they shall reap the whirlwind. They shall have no standing harvest; The ear shall yield no meal; If perchance it yield, strangers shall devour it.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Israel is swallowed up; Soon shall they become among the nations As a vessel which no one desireth.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 For they have gone up to Assyria, Like a solitary wild-ass; Ephraim hireth lovers;
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 But though they hire among the nations, Soon will I gather the nations against them; Then shall they rest a little while from the burden of their king, and their princes!
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 Ephraim hath built many altars for sin, Therefore shall he have altars for sin.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 Though I write for him many laws, They are accounted as a strange thing;
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 As to the sacrifices which they should offer me, they slay flesh and eat it; Jehovah hath no pleasure in them. Now will he remember their iniquity, And punish their sins; To Egypt shall they return.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 For Israel hath forgotten his Maker, and builded palaces, And Judah hath multiplied fenced cities; But I will send a fire upon his cities, And it shall devour his palaces.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”