< Hebrews 5 >

1 For every high-priest, being taken from among men, is appointed for men in things pertaining to God, that he may offer both gifts and sacrifices for sins;
Akan zaɓi kowane babban firist daga cikin mutane ne, akan kuma naɗa shi domin yă wakilce su a kan al’amuran Allah, domin yă miƙa kyautai da hadayu saboda zunubai.
2 being able to be forbearing toward the ignorant and the erring, since he himself also is compassed with infirmity;
Da yake babban firist ɗin mai kāsawa ne, yana iya bin da jahilai da kuma waɗanda suka kauce hanya, a hankali.
3 and by reason of this infirmity he must, as for the people, so also for himself, offer sacrifice for sins.
Shi ya sa dole yă miƙa hadayu domin zunubansa, da kuma domin zunuban mutane.
4 And no one taketh this honor to himself, but when called by God, as was Aaron.
Ba wanda yakan kai kansa a wannan matsayi mai girma; sai ko Allah ya kira shi, kamar yadda aka yi wa Haruna.
5 Thus Christ did not glorify himself to be made high-priest, but he who said to him, “Thou art my Son, I this day have begotten thee;”
Haka ma Kiristi bai kai kansa neman ɗaukaka na zama babban firist ba. Allah ne dai ya ce masa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka.”
6 as also he saith in another place, “Thou art a priest for ever, after the order of Melchizedek.” (aiōn g165)
Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn g165)
7 Who in the days of his flesh, when he had offered up prayers and supplications, with strong crying and tears, to him that was able to save him from death, and was heard by reason of his godly reverence,
A lokacin da Yesu ya yi rayuwa a duniya, ya yi addu’o’i da roƙe-roƙe tare da kuka mai zafi da kuma hawaye ga wannan wanda yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa ji shi saboda tsananin bangirman da ya yi.
8 though a son yet learned his obedience from what he suffered;
Ko da yake shi ɗa ne, ya yi biyayya ta wurin shan wahala
9 and being perfected became the author of everlasting salvation to all who obey him, (aiōnios g166)
kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios g166)
10 being addressed by God as high-priest after the order of Melchizedek.
Allah kuwa ya naɗa shi yă zama babban firist, bisa ga tsarin Melkizedek.
11 Of whom we have much to say, and hard to be explained, seeing ye have become dull of hearing.
Muna da abubuwa masu yawa da za mu faɗa game da wannan batu, sai dai yana da wuya a bayyana, da yake ba ku da saurin ganewa.
12 For while on account of the length of time ye ought to be teachers, ye again have need that some one should teach you the first elements of the oracles of God, and are become such as have need of milk, and not of solid food.
Gaskiya, a yanzu ya kamata a ce kun zama malamai, sai ga shi kuna bukatar wani yă sāke koya muku abubuwa masu sauƙi game da abin da Allah ya faɗa. Kuna bukatar madara, ba abinci mai kauri ba!
13 For every one that feedeth on milk is unacquainted with the word of righteousness; for he is a babe;
Duk wanda yake rayuwa a kan madara, shi kamar jariri ne har yanzu, kuma bai san ainihi mene ne ya dace ba.
14 but solid food belongs to those who are of full age, who by use have their senses exercised to discern both good and evil.
Amma abinci mai kauri na balagaggu ne, waɗanda suka hori kansu don su bambanta tsakanin nagarta da mugunta.

< Hebrews 5 >